Tirkashi: An Samu Kungiyar da Za Ta ba Janar Musa Hujjoji kan Zarge Zargen da Ya Yi Wa El Rufai
- Kungiyar Middle Belt Forum ta bukaci Christopher Musa ya yi watsi da buƙatar iyalan Nasir El-Rufai ta janye zargin da aka yi wa tsohon gwamnan
- Iyalan El-Rufai sun ba Musa wa’adin kwanaki bakwai ya gabatar da hujjoji kan zargin shirya kisan mutane a Kudancin Kaduna
- MBF ta ce tana da isassun hujjoji da za su goyi bayan kalaman ministan, yayin da El-Rufai ya yi barazanar kai ƙara kan Janar Musa
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Kaduna - Kungiyar Middle Belt Forum (MBF) ta bukaci Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), da ya yi watsi da buƙatar iyalan tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai.
Kungiyar ta ce Musa bai kamata ya janye zargin cewa El-Rufai yana da hannu wajen kashe-kashen da suka faru a Kudancin Kaduna a lokacin mulkinsa ba.

Source: Facebook
Mai magana da yawun MBF, Luka Binniyat, ya ce kungiyar tana da isassun hujjojin da za su tabbatar da zargin da ministan ya yi, cewar rahoton jaridar Leadership.
Iyalan El-Rufai sun ba Musa kwanaki 7
A baya, iyalan El-Rufai sun bai wa Janar Musa wa’adin kwanaki bakwai da ya gabatar da hujjojin da ke tabbatar da zargin cewa tsohon gwamnan ya shirya kisan mutane a Kudancin Kaduna.
Iyalan sun kuma yi barazanar ɗaukar matakin shari’a a kan ministan idan ya gaza tabbatar da zargin ko kuma ya janye shi tare da ba da haƙuri a bainar jama’a cikin wa’adin da suka kayyade.
MBF ta goyi bayan Janar Musa
Sai dai MBF ta ce ya kamata Janar Musa ya tsaya kan kalamansa maimakon janyewa ko neman afuwa.
Luka Binniyat ya ce MBF tana goyon bayan ministan kan kalaman da ya yi game da El-Rufai.
“Middle Belt Forum tana tsaye tsayin daka tare da ministan tsaro kan zarge-zargen da ya yi wa Rufai kwanan nan. Abin da ministan ya fada gaskiya ne, kuma muna da isassun hujjojin da za su goyi bayansa.” In ji shi.

Kara karanta wannan
Janar Christopher Musa ya kira ruwa, lauyoyin El Rufai sun nemi N10bn da wasu bukatu
Ya ƙara da cewa bai kamata Janar Musa ya janye kalamansa ko ya nemi afuwa ba.
Kungiyar ta kuma yi zargin cewa ayyuka da kalaman El-Rufai, ko rashin ɗaukar mataki a lokacin da ya dace, sun taimaka wajen ƙara yawaitar kashe-kashen jama’a a Kudancin Kaduna.
MBF ta yi wani ƙarin zargi mai tsanani cewa El-Rufai ya kamata ya fuskanci tuhume-tuhume a gaban Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC) kan zargin aikata laifukan cin zarafin bil’adama.
Janar Musa bai mayar da martani ba
Har zuwa lokacin kammala rahoton, Ministan Tsaro, Christopher Musa, bai fito ya mayar da martani kan buƙatun iyalan El-Rufai ko barazanar shari’ar ba.
Haka kuma, Leah Katung-Babatunde, mataimakiyar Janar Musa ta musamman kan harkokin yaɗa labarai, ba ta amsa saƙonni ko kiran waya da aka yi mata domin jin ta’addamar da ministan kan lamarin ba.

Source: Facebook
Kungiyar Arewa ta goyi bayan Janar Musa
A wani labarin kuma, kun ji cewa kungiyar Coalition of Northern Elders for Peace and Development, CNEEPD, ta goyi bayan Ministan Tsaro, Christopher Musa kan sukar Nasir El-Rufai.
Ƙungiyar ta ce kalaman Musa sun bayyana abin da ta kira gaskiyar gwamnatin El-Rufai, wadda ta shafe shekaru takwas tana mulkin Kaduna.
Asali: Legit.ng
