Zargin Ta’addanci: Sanata Buba Ya Shiga Kotu da Matashi da Ya Yi Tone Tone
- Sanata Shehu Buba Umar ya bukaci hukumomi su gudanar da bincike kan zarge-zargen da ake masa na alaƙa da ’yan ta’adda
- Sanatan ya kalubalanci Hassan da ya gabatar da duk wata hujja da yake da ita ga hukumomin tsaro domin gudanar da bincike na doka
- Masu goyon bayan Shehu Buba sun ce ba za su amince da amfani da kafafen sada zumunta wajen yada zarge-zargen da ba a tabbatar ba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja — Sanata Shehu Buba Umar ya bukaci a dauki matakin doka kan zarge-zargen da ake danganta shi da ayyukan ’yan ta’adda.
Sanatan ya kuma kalubalanci wanda ya yi zargin, Hassan, da ya gabatar da hujjojin da yake da su ga hukumomin da suka dace.

Source: Facebook
Hakan na cikin wasu takardun korafi da sanatan ya fitar wanda shafin yada manufofinsa, Mujaddadi TV ya wallafa a Facebook.
Matsayar sanatan kan zarginsa da ake yi
Matsayar sanatan ta biyo bayan yaduwar wasu bidiyoyi da ake zargin suna da alaƙa da shi, da kuma ikirarin Hassan.
Hassan ya yi ikirarin cewa Shehu Buba na da alaƙa da ’yan ta’adda, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a.
A cewar wata sanarwa da magoya bayan sanatan suka fitar, an gabatar da korafe-korafe kan zarge-zargen da bidiyoyin ga hukumomin tsaro tun shekarar 2025.
Sanarwar ta ce Hassan, wanda ke ci gaba da yin zarge-zargen ta kafafen yaɗa labarai, bai bayyana gaban hukumomin tsaro ba.
An ce hakan ya faru ne duk da cewa rahotanni sun nuna an gayyace shi domin ya gabatar da hujjojin da yake da su.
Saboda haka, sanatan da magoya bayansa sun bukaci hukumomin da suka dace su binciki zarge-zargen tare da daukar matakin doka.
Sanarwar ta ce: “Ba mu da wata matsala da bincike ko tambayoyi daga hukumomin da suka dace.”
Ta kuma jaddada cewa duk wanda yake da sahihiyar hujja kan sanatan ya kamata ya gabatar da ita a hukumomin tsaro.
Masu goyon bayan sanatan sun ce bai kamata a gudanar da zarge-zarge masu tsanani irin wadannan ta kafafen sada zumunta ba.
Sun ce ya kamata a bi hanyoyin doka da binciken hukumomi da aka tanada domin tabbatar da gaskiyar zarge-zargen.

Source: Facebook
Zargin da Shehu Buba ke yi wa Hassan
Sanarwar ta kuma zargi Hassan da kokarin lalata mutuncin sanatan ta hanyar abin da ta bayyana a matsayin zarge-zargen alaka da ta'addanci.
Sanarwar ta bukaci Hassan ya gabatar da duk wata hujja da yake da ita ga hukumomin da suka dace domin gudanar da bincike.
Ta ce bincike na hukuma zai samar da damar tantance zarge-zargen cikin gaskiya da kuma ba tare da son zuciya ba.
Sanarwar ta ƙara da cewa:
“Ba za mu amince da amfani da zarge-zargen da ba su da tushe, ɓata suna ko yada bayanan da ba a tabbatar ba a matsayin kayan siyasa ba.”
Ta ce ba za a yi amfani da irin wadannan zarge-zarge wajen bata sunan wani mutum saboda dalilan siyasa ba.
MURIC ta kare Sanata Shehu Buba
An ji cewa Kungiyar MURIC ta yi Allah wadai da zargin Sanata Shehu Buba da ake yi da ɗaukar nauyin ta'addanci a Najeriya.
Kungiyar kare hakkin Musulmai ta ce babu hujjoji kan zargin sanatan wanda ya kasance haziki da ke hidimtawa al'ummarsa.
Hakan ya biyo bayan zargin da gwamnatin jihar Bauchi ta yi kan sanatan da daukar nauyin dan ta'adda zuwa aikin hajji.
Asali: Legit.ng


