Ranar da Tsohon Gwamna Ya Bar APC, EFCC Ta Tado Zancen Neman Sa kan Zargin Satar $14m

Ranar da Tsohon Gwamna Ya Bar APC, EFCC Ta Tado Zancen Neman Sa kan Zargin Satar $14m

  • Hukumar EFCC ta jaddada cewa har yanzu tana neman Timipre Sylva ruwa a jallo domin ya amsa tambayoyi
  • Tsohon ministan man ya sanar da ficewarsa daga jam'iyyar APC yayin da ya zargi APC da karya alkawuran da ta yi
  • Ganin Sylva ya aika da takardar murabus dinsa zuwa EFCC, an tuna masa ana zarginsa da karktar da $14m

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M Malumfashi ya shafe shekaru 10 yana kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada

Abuja - Hukumar EFCC mai yaki da rashin gaskiya, tana neman Timipre Sylva ruwa a jallo saboda zargin satar kudi.

Ana tuhumar tsohon gwamnan na jihar Bayelsa da satar $14.86m don haka EFCC ta bukaci ya kawo kan shi da kan shi.

Sylva
Timipre Sylva da ake nema da hoton tambarin EFCC a Najeryiya Hoto: Getty Images/EFCC Nigeria
Source: UGC

Ana neman Timipre Sylva a ofishin EFCC

Rahoto ya fito daga jaridar Punch cewa an bukaci ‘dan siyasar ya kai kan shi gaban hukumar domin ya amsa tambayoyi.

Kara karanta wannan

Tsohon gwamnan da ake zargi da shirya wa Tinubu juyin mulki ya fita a APC

Kakakin EFCC na kasa, Dele Oyewale ya bayyana wannan a ranar Litinin a kokarin maida wa tsohon gwamnan martani.

Timipre Sylva ya zargi hukumar yaki da rashin gaskiyar da zama tamkar wani bangare na jam’iyyar APC mai mulki a kasa.

Hikumar EFCC tana neman Sylva har gobe

Mista Dele Oyewale ya shaida wa duniya cewa yanzu haka aka neman Cif Sylva kuma ana bukatar ya kawo kan shi hedikwatar EFCC.

Da ya tashi barin APC, ‘dan siyasar ya rubuta a takardar murabus dinsa cewa jam’iyyar da su ne suka kafa ta, ta saki layi a halin yanzu.

Sannan kuma ya hada da EFCC a wasikar, yana sanar da ita wannan mataki da ya dauka.

Wasikar tsohon gwamnan ta tsokano EFCC

Ko da aka nemi jin dalilin ambatar hukumar EFCC a wasikar da ya fitar, Jaridar The Sun ta rahoto shi yana cewa da gan-gan da ya yi hakan.

Kara karanta wannan

Da gaske hukumar Hisbah ta hana Kiristoci gudanar da ibada a Sokoto

Ana zargin hukumomin yaki da rashin gaskiya da siyasantar da binciken da suke yi a Najeriya.

Timipre Sylva da ake nema da hoton tambarin EFCC a Najeryiya Hoto: Getty Images
Tsohon ministan mai, Timipre SylvaHoto: Getty Images
Source: Getty Images

Tsohon karamin ministan na harkokin man fetur ya kuma ce yana sane cewa barin jam’iyyar zai iya jefa shi da yaransa na siyasa a matsala.

Duk wannan abin da aka yi har ake zarginsa da hannu a shirya wa gwamnatin Bola Tinubu juyin mulki, ‘dan siyasar yana kasar waje.

Sai dai duk da yiwuwar bita-da-kullin, Cif Sylva ya yi sallama da jam’iyyar APC mai-ci.

APC ta rasa tsohon gwamnan Bayelsa

Tsohon gwamnan jihar Bayelsa, Timipre Sylva, ya sanar da murabus dinsa daga jam’iyyar APC mai mulki ba tare da wani bata lokaci ba.

Sylva ya bayyana cewa ya dauki wannan mataki ne saboda yadda jam'iyyar ta karkata daga manufofi da akidojin da aka kafa ta a kansu.

Da alama dai murabus dinsa na zuwa ne sakamakon zargin da ake yi masa na hannu a shirin juyin mulki da kuma zargin karkatar da kudi

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng