Shugaba Tinubu Ya Shilla Kasashen Waje bayan Fara Yakin Neman Zaben 2027

Shugaba Tinubu Ya Shilla Kasashen Waje bayan Fara Yakin Neman Zaben 2027

  • Shugaba Bola Tinubu ya bar babban birnin tarayya Abuja zuwa Turai domin fara hutun makonni uku na shekara
  • Birnin London da ke kasar Birtaniya ne zangon farko na hutun shugaban kasar wanda ke neman wa'adi na biyu a zaben 2027
  • Ana sa ran Tinubu zai dawo Najeriya bayan hutun domin shiga yakin neman zaben shugaban kasa na Janairu 2027

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya fara hutun makonni uku a nahiyar Turai.

Shugaba Tinubu ya tafi hutun ne a matsayin wani bangare na hutun shekara-shekara da yake da hakki a kai.

Shugaba Tinubu ya tafi hutu
Shugaba Bola Tinubu yana dawo hannu daga jirgin sama Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan yada labarai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi, 30 ga watan Agustan 2026 a shafinsa na X.

Kara karanta wannan

Shugabannin kwamitin yakin zabe da aka yi kafin Abdulaziz Yari daga 1999 zuwa 2027

Birnin London ne zangon farko

A cewar Onanuga, Tinubu zai bar Abuja zuwa Turai a ranar Lahadi domin fara hutunsa na tsawon makonni uku.

Ya ce zangon farko na shugaban kasar zai kasance a London, Birtaniya, inda zai fara hutun aiki.

Sanarwar da Bayo Onanuga ya fitar ta ce hutun na daga cikin hutun shekara-shekara na shugaban kasa.

Zai dawo domin yakin neman zabe

Onanuga ya bayyana cewa ana sa ran Tinubu zai koma Najeriya bayan kammala hutun domin shiga harkokin yakin neman zaben shugaban kasa na Janairu 2027.

Yakin neman zaben na zuwa ne yayin da jam’iyyun siyasa da ‘yan takararsu ke kara shirin tunkarar babban zaben da ake sa ran zai kasance mai tsauri.

Tinubu na neman wa’adi na biyu a matsayin shugaban Najeriya, yayin da ‘yan takara daga jam’iyyun adawa ke kokarin hada karfi domin kalubalantar jam’iyyar APC a zaben 2027.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng