Kwana Ya Kare: Tsohon Sanata daga Jihar Borno Ya Riga Mu Gidan Gaskiya
Borno, Nigeria - Tsohon Sanatan da ya wakilci mazabar Borno ta Tsakiya a Majalisar dattawan Najeriya, Kaka Mallam Yale, ya riga mu gidan gaskiya bayan fama da rashin lafiya.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Rahotanni sun bayyana cewa Sanata Kaka Yale ya rasu ne a safiyar Juma’a, 28 ga watan Agusta, 2026 a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri da ke birnin Maiduguri na jihar Borno yayin da yake karbar magani.

Source: Facebook
An sanar da rasuwar Sanata Kaka Yale
Daya daga cikin ’ya’yansa, Ibrahim Yale, ne ya tabbatar wa da jaridar PUNCH da rasuwar mahaifinsu a wata tattaunawa ta wayar tarho da aka yi da shi ranar Juma’a.
“Eh, ni ne dan cikinsa, mahaifinmu, Kaka Yale, ya rasu a yau (Juma’a),” in ji shi.
Sanata Kaka Mallam Yale ya wakilci mazabar Borno ta Tsakiya a Majalisar Dattawa daga shekarar 2007 zuwa 2011 karkashin jam’iyyar ANPP.
Karin bayani na nan tafe...
Asali: Legit.ng