Kwana Ya Kare: Tsohon Sanata daga Jihar Borno Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

Kwana Ya Kare: Tsohon Sanata daga Jihar Borno Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

Borno, Nigeria - Tsohon Sanatan da ya wakilci mazabar Borno ta Tsakiya a Majalisar dattawan Najeriya, Kaka Mallam Yale, ya riga mu gidan gaskiya bayan fama da rashin lafiya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Rahotanni sun bayyana cewa Sanata Kaka Yale ya rasu ne a safiyar Juma’a, 28 ga watan Agusta, 2026 a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri da ke birnin Maiduguri na jihar Borno yayin da yake karbar magani.

Kaka Mallam Yale
Tsohon sansta da ya wakilci mazabar Borno ta Tsakiya, Sanata Kaka Mallam Yale Hoto: Muhammad Wakil
Source: Facebook

An sanar da rasuwar Sanata Kaka Yale

Daya daga cikin ’ya’yansa, Ibrahim Yale, ne ya tabbatar wa da jaridar PUNCH da rasuwar mahaifinsu a wata tattaunawa ta wayar tarho da aka yi da shi ranar Juma’a.

“Eh, ni ne dan cikinsa, mahaifinmu, Kaka Yale, ya rasu a yau (Juma’a),” in ji shi.

Sanata Kaka Mallam Yale ya wakilci mazabar Borno ta Tsakiya a Majalisar Dattawa daga shekarar 2007 zuwa 2011 karkashin jam’iyyar ANPP.

Karin bayani na nan tafe...

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262