An Yi Rashi: Shugaban Hukumar Kidaya Ta Ƙasa, NPC Ya Yi Bankwana da Duniya

An Yi Rashi: Shugaban Hukumar Kidaya Ta Ƙasa, NPC Ya Yi Bankwana da Duniya

  • Shugaban Hukumar Kidaya ta Kasa, NPC ya rasu ranar Juma’a, 28 ga Agusta 2026, bayan fama da gajeriyar rashin lafiya
  • Labarin rasuwarsa ya isa Minna, babban birnin Niger, lokacin sallar Juma’a, lamarin da ya jefa ‘yan siyasa da abokan huldarsa cikin jimami
  • Mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai, Stanley Nwosu, ya tabbatar da rasuwar, yana mai cewa Wushishi ya rasu bayan gajeriyar rashin lafiya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Minna, Niger - Rahotanni sun bayyana cewa shugaban hukumar kidaya ta kasa, NPC ya riga mu gidan gaskiya.

Dakta Aminu Wushishi ya rasu ranar Juma’a, 28 ga Agusta 2026, bayan fama da gajeriyar rashin lafiya.

Shugaban hukumar kidaya, Wushishi ya rasu
Taswirar jihar Niger da Aminu Wushishi ya fito. Hoto: Legit.
Source: Original

Labarin rasuwarsa ya isa Minna, babban birnin Niger, a daidai lokacin sallar Juma’a, lamarin da ya jefa abokansa da ‘yan siyasa cikin jimami, cewar Vanguard.

Kara karanta wannan

Harald V: Babban sarkin da ya fi tsufa a Turai ya rasu bayan shekara 35 a karagar mulki

Wushishi, wanda ya taba zama Sakataren jam’iyyar Peoples Democratic Party, PDP, reshen Niger, an ce ya yi fama da rashin lafiya na wani dan lokaci kafin rasuwarsa.

Mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Stanley Nwosu, ya tabbatar wa Vanguard da rasuwar shugaban NPC.

Ya ce:

“Eh, gaskiya ne. Shugaban NPC ya rasu bayan gajeriyar rashin lafiya."

Ya zuwa lokacin da aka hada wannan rahoto, har yanzu ana jiran karin bayani kan musabbabin rasuwarsa da kuma shirye-shiryen jana’izarsa.

Karin bayani na tafe.....

Tsohon mataimakin gwamnan Bauchi ya rasu

A baya, an ji cewa mun samu labarin rasuwar tsohon gwamnan jihar Bauchi kuma wazirin Katagum, Arch. Audu Sule Katagum a safiyar yau Asabar, 20 ga Yuni, 2026.

Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed ya mika sakon ta'aziyya ga iyalan marigayin, tare da addu'ar Allah Ya masa rahama.

Ya bayyana marigayi Wazirin Katagum a matsayin shugaba kuma tsayayyen dattijo, wanda rashinsa babban gibi ne ga jihar Bauchi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.