Za a Cigaba da Shagalin Mauludi a Kano, Abba Ya ba da Hutun Takutaha
- Gwamnatin jihar Kano ta ayyana ranar Talata, 1 ga watan Satumban 2026, a matsayin ranar hutu domin gudanar da bukukuwan Takutaha
- Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da hutun domin bai wa mazauna Kano damar halartar wannan gagarumin biki a fadin jihar
- Gwamnatin Kano ta bukaci ma'aikata da al'umma su yi amfani da ranar wajen addu'o'in neman zaman lafiya da ci gaban Kano da Najeriya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf Kari yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Jihar Kano – Gwamnatin jihar Kano ta ayyana ranar Talata, 1 ga watan Satumban 2026, a matsayin ranar hutu domin bai wa mazauna jihar damar gudanar da bukukuwan mauludin Takutaha.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwa mai lamba 7/2026, wadda Babban Sakataren Hukumar Kula da Ma'aikata a jihar Kano, Abba A. Danguguwa, ya sanya wa hannu a madadin Shugaban Ma'aikatan Gwamnatin Jihar.

Source: Facebook
Za a yi hutunTakutaha
Daily Trust ta wallafa cewa sanarwar ta ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da ayyana ranar hutun, wadda ta yi daidai da ranar 19 ga watan Rabi'ul Awwal, 1448 bayan hijira.
An kuma tura sanarwar ga manyan jami'an gwamnati, ciki har da kwamishinoni, manyan sakatarori da shugabannin hukumomin gwamnati domin su sanar da ma'aikatan da abin ya shafa..
An nemi jama'a su yi addu'a
Gwamnatin ta bukaci ma'aikatan gwamnati da sauran al'umma su yi amfani da ranar hutun wajen addu'a, tare da neman albarkar Allah domin samun zaman lafiya da wadata a Kano da Najeriya baki daya.
Sai dai sanarwar ta ce hukumomin da ke gudanar da ayyuka masu muhimmanci da ba za su iya tsayawa ba za su ci gaba da gudanar da aikinsu kamar yadda aka saba.
Takutaha tsohuwar al'ada ce da ake gudanarwa duk ranar 19 ga watan Rabi'ul Awwal, inda ake danganta bikin da ranar suna bayan haihuwar Annabi Muhammad (SAW).

Source: Facebook
Yadda ake Takutaha a Kano
Bikin na jawo dimbin jama'a daga wurare daban-daban, inda mahalarta ke sanya kaya masu launuka tare da rera yabon Annabi Muhammad (SAW) yayin da suke tattaki a sassa daban-daban na tsohon birnin Kano.
Wasu daga cikin mahalartan kan nufi tsaunukan Dala da Goron Dutse, inda suke hawa domin gudanar da bukukuwa, cin abinci tare da kallon wasu wasannin da suka shafi addini da al'adu.
Tun da farko, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bukaci musulmi su yi koyi da kyawawan halaye da dabi'un Annabi Muhammad (SAW) yayin gudanar da bukukuwan Maulud na bana.
Abba ya yabi Sheikh Jingir
A wani labarin, mun ruwaito cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano da wasu gwamnoni sun yaba wa shugaban Majalisar Malamai ta Jama'atu Izalatil Bid'a Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), Sheikh Sani Yahaya Jingir.
Gwamnonin sun yaba masa kan kokarinsa na inganta hadin kai, zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin musulmi da sauran 'yan Najeriya a wani taron kasa da aka gudanar a birnin Jos na jihar Plateau.
A yayin taron, JIBWIS ta kuma bukaci mambobinta a fadin Najeriya su goyi bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Mataimakinsa, Kashim Shettima, tare da zaben su a babban zaben shugaban kasa na shekarar 2027.
Asali: Legit.ng

