"Amma Ya Tsane Ni"; Atiku Ya Fallasa Yadda Ya Tseratar da Obasanjo daga Mutuwa
- Atiku Abubakar ya ce ya ceci Olusegun Obasanjo daga wata allura da ake zargin za ta iya kashe shi a gidan yari
- Dan takarar shugaban kasa na African Democratic Congress (ADC) ya ce ya tona asirin shirin tare da gargadin Obasanjo kada a yi masa allurar
- Tsohon mataimakin shugaban kasar ya kuma ce an yi irin wannan yunkuri ga marigayi Janar Shehu Musa Yar’Adua
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Dan takarar shugaban kasa na African Democratic Congress (ADC), Atiku Abubakar, ya bayyana yadda ya ce ya ceci tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo daga wata allura da ake zargin an shirya yi masa a gidan yari.
Atiku ya ce ya fallasa bayanan shirin yin allurar tare da gargadin Obasanjo kada ya amince a yi masa ita.

Source: Facebook
Atiku Abubakar ya bayyana hakan ne yayin da yake magana da manema labarai a wata hira da aka yi da shi wadda ya sanya a shafinsa na Facebook.
Abin da Atiku ya ce ya faru
Tsohon mataimakin shugaban kasar ya ce an yi irin wannan shiri kan marigayi Janar Shehu Musa Yar’Adua.
“Na ceci ran Obasanjo a gidan yari ta hanyar tona bayanan wata allura da ake shirin yi masa wadda za ta iya kashe shi.
“Sun yi irin haka ga Yar’Adua, kuma lokacin da na samu labarin cewa suna shirin yi masa, na gargade shi kada ya bari a yi masa allurar."
“Yanzu yana son duniya ta tsane ni saboda na yi adawa da burinsa na wa’adin mulki na uku,” in ji Atiku.
Wannan ikirari na Atiku ba a gabatar da shi a matsayin tabbataccen binciken da ya tabbatar da cewa an yi wani shiri na kashe Obasanjo ta hanyar allura ba. Bayanin nasa ne kan abin da ya ce ya faru.
An kai Obasanjo gidan yari
Gwamnatin mulkin soja ta Sani Abacha ta kama tare da daure Obasanjo a shekarar 1995 bayan da aka same shi da laifin hannu a wani zargin yunkurin juyin mulki.

Kara karanta wannan
Abin da Atiku zai yi don magance rashin tsaro cikin kwana 100 idan ya zama shugaban kasa
Obasanjo ya ci gaba da zama a gidan yari har zuwa watan Yuni na shekarar 1998, bayan rasuwar Abacha da kuma fara wani tsari na komawa mulkin farar hula.
Daga baya Obasanjo ya zama shugaban Najeriya a shekarar 1999, yayin da Atiku ya kasance mataimakinsa.
Atiku ya sake tuna alakarsa da Obasanjo ne a matsayin wani bangare na martanin da yake mayarwa kan sukar da tsohon shugaban kasar ke yi masa.

Source: Facebook
Dangantakarsu ta tabarbare
Dangantakar mutanen biyu daga baya ta tabarbare, musamman kan yunkurin Obasanjo mai cike da ce-ce-ku-ce na tsawaita wa’adin mulkinsa fiye da wa’adi biyu da kundin tsarin mulki ya amince da su.
Atiku ya yi adawa da shirin wa’adin mulki na uku, wanda ya nemi sauye-sauyen kundin tsarin mulki da za su ba Obasanjo damar ci gaba da mulki bayan shekarar 2007.
Daga karshe shirin ya fadi ne bayan fuskantar gagarumar adawa a Majalisar Dokoki ta Kasa.
Atiku ya sha bayyana adawarsa da shirin a matsayin kokarin kare dimokuradiyyar kundin tsarin mulkin Najeriya.
An gargadi Obasanjo kan Atiku
A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon gwamnan jihar Cross Rivers, Donald Duke, ya bayyana yadda Ibrahim Babangida ya gargadi tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo kan mataimakinsa Atiku Abubakar.
Donald Duke ya bayyana cewa Janar Babangida ya taba gargadin Obasanjo da ka da ya harda da Atiku wanda a lokacin yake matsayin mataimakinsa.
Asali: Legit.ng
