Mutane Sun Mutu da Gine Gine 2 Suka Rufta kan Daliban Islamiyya da Ma'aikata a Kano

Mutane Sun Mutu da Gine Gine 2 Suka Rufta kan Daliban Islamiyya da Ma'aikata a Kano

  • Mutane biyar, ciki har da ma’aikatan gini huɗu da ɗalibar makarantar Islamiyya, sun mutu sakamakon ruftawar wasu gine-gine a Kano
  • Rahoto ya nuna cewa lamarin ya faru ne a Gaida da ke ƙaramar hukumar Kumbotso da Kurna a ƙaramar hukumar Fagge ranar Asabar
  • Ma’aikatan hukumar kashe gobara sun ceto wasu mutane 10 da hatsarin ya rutsa da su, amma biyar sun mutu daga baya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Mutane biyar, ciki har da leburori huɗu da ɗalibin makarantar Islamiyya, sun mutu a wasu gine-gine biyu da suka ruguje a jihar Kano.

Hatsarin ruftawar gine-ginen ya faru ne ranar Asabar da ta wuce a Gaida da ke ƙaramar hukumar Kumbotso da Kurna da ke ƙaramar hukumar Fagge ta jihar.

Kano.
Taswirar jihar Kano da ke Arewacin Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Leadership ta ruwaito cews jami’in hulɗa da jama’a na Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, Saminu Yusif, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.

Kara karanta wannan

Abin tausayi: Hatsarin jirgi ya rutsa da manoma a hanyar zuwa gonakinsu a Najeriya

Gini ya lashe mutane 4 a Kano

Yusif ya ce hatsarin farko ya faru da misalin ƙarfe 2.34 na rana a Gaida, kusa da gidsn mai na Salbas, inda wani ginin da ake ginawa wanda bai kammala ba ya ruguje kan ma’aikata shida.

Ya ce an ceto biyu daga cikin ma’aikatan, Muhammad Hassan mai shekaru 17 da Khalid Abubakar mai shekaru 19, da ransu.

Sai dai ma’aikatan kashe gobarar sun fito da wasu huɗu daga cikin ginin a sume, kuma daga baya aka tabbatar da mutuwarsu.

An bayyana sunayen mamatan da Sunusi Surajo mai shekaru 18, Bashir Ibrahim mai shekaru 20, Ibrahim Ibrahim mai shekaru 25 da Abubakar mai shekaru 30.

A cewarsa, an kwashe dukkan mutanen shida zuwa Asibitin Kwararru na Murtala Muhammad, inda aka miƙa su ga ‘yan sanda.

Ɗalibar Islamiyya ta mutu

Yusif ya ce lamari na biyu ya faru ne bayan kusan mintuna shida a Kurna, a bayan makarantar firamare, inda wani ginin makarantar Islamiyya mai suna Khadija Idris Bala ya ruguje.

Kara karanta wannan

EFCC ta kai wani mutum kotu kan zargin baba kere da N56m na kudin aikin hajji

Ya ce ɗalibai tara ne abin ya shafa, inda aka ceto takwas da ransu, amma Khadija Muhammad mai shekaru 14, wadda aka ceto a sume, ta mutu daga baya.

An bayyana sunayen waɗanda suka tsira da Hassana Isah, Usaina Isah, Zulaihat M. Gambo, Nawara Yahaya, Nusaiba Isah, Hasiya Munir, Khadija Isah da Hadiza Haruna.

Kakakin hukumar kashe gobara ya ce an miƙa waɗanda lamarin ya rutsa da su ga shugaban makarantar, Muhammad Gambo Usman.

Ruftawar gini.
Daya daga cikin gine-ginen da suka ruguje a jihar Kano Hoto: Ma'aruf Rukayyat
Source: Facebook

Ana binciken dalilin ruftawar gini

Hukumar Kashe Gobara ta ce ana ci gaba da binciken musabbabin rushewar gine-ginen biyu, kamar yadda Daily Post ta kawo.

Yusif ya buƙaci masu gine-gine, ‘yan kwangila da leburori su kiyaye dokokin tsaro da ƙa’idojin gini, musamman a lokacin damina, domin hana sake samun rushewar gine-gine da asarar rayuka.

Gini ya yi ajalin uwa da yaranta 2

A baya, kun ji wata mata mai shekara 35 da ’ya’yanta biyu sun mutu bayan wani gini da ake ginawa ya rufta kan gidansu a jihar Kaduna.

Mijin matar, Abubakar Abba Haruna, ya ce ba ya gida lokacin da lamarin ya faru, domin ya kwana a gidan dayar matarsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262