'Yan Najeriya na Cikin Alheri, An Turo Musu Tallafin Fiye da Naira Biliyan 40 daga Kasar Waje

'Yan Najeriya na Cikin Alheri, An Turo Musu Tallafin Fiye da Naira Biliyan 40 daga Kasar Waje

  • Gwamnatin kasar China ta bai wa Najeriya tallafin Yuan miliyan 200, kwatankwacin kimanin Naira biliyan 40
  • Rahoto ya nuna cewa za a yi amfani da tallafin wajen aiwatar da ayyukan da gwamnatocin kasashen biyu suka amince da su
  • Kasashen biyu sun ce suna son kara zurfafa hadin gwiwar diflomasiyya da bunkasa tattalin arziki

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Gwamnatin China ta yi alkawarin bai wa Najeriya tallafin yuan miliyan 200, wanda ya haura Naira biliyan 40 domin taimakawa kasar wajen aiwatar da wasu ayyukan ci gaba ga jama'arta

An bayyana hakan ne ranar Alhamis bayan da Jakadan China a Najeriya, Yu Dunhai, ya gana da Babban Sakataren Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya, Dr Ahmed Dunoma, a Abuja.

Shugaban kasar China.
Shugaban kasar China, Xi Jinping a fadar gwamnatinsa Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Leadershi ta ruwasito cewa wata sanarwa da Ofishin Jakadancin China a Najeriya ya fitar ta ce tallafin na daga cikin matakan karfafa alakar diflomasiyya da hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.

Kara karanta wannan

Gwamntin Tinubu na neman 'ƙaryata' rahoton da ƙasar Amurka ta fitar kan Najeriya

China ta dauko tarihin shekaru 55

Jakadan Yu ya ce a cikin shekaru 55 da suka gabata tun bayan kulla huldar diflomasiyya tsakanin China da Najeriya, kasashen biyu sun kasance cikin sahun gaba wajen karfafa dangantakar China da kasashen Afirka.

Ya ce a shekarun baya-bayan nan, karkashin jagorancin Shugaban China, Xi Jinping, da Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, dangantakar hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu ta shiga wani sabon mataki na ci gaba mai inganci.

A cewarsa, China da Najeriya sun ci gaba da tuntubar juna tare da aiki tare wajen aiwatar da yarjejeniyoyin da shugabannin kasashen biyu suka cimma.

Abubuwan da za a yiwa yan Najeriya

Jakadan China ya ce:

“Domin kara tallafa wa ci gaban kasa da bunkasar tattalin arzikin Najeriya, China za ta samar da tallafin yuan miliyan 200 ga Najeriya domin aiwatar da ayyukan da gwamnatocin kasashen biyu suka amince da su.”

Kara karanta wannan

Hankalin Tinubu ya koma kan matatun mai bayan karɓar tawagar NUPENG

Ya ce wannan mataki na daga cikin kokarin China na kara tallafa wa Najeriya wajen cimma manufofin ci gabanta da bunkasa tattalin arzikinta.

Najeriya ta yaba wa China

A nasa bangaren, Sakataren Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya, Dr Ahmed Dunoma, ya yabawa China kan irin tallafin da take bai wa Najeriya wajen bunkasa tattalin arziki da zamantakewar al’umma.

Dunoma ya ce tallafin ya nuna irin nauyin da China ke dauka a matsayin babbar kasa, sannan ya kara tabbatar da zurfin zumunci da ke tsakanin Najeriya da China.

Tinubu.
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu yana gaisawa da Shugaba Xi Jinping a taron China da kasashen Afirka da ya gudana a birnin Beijing Hoto: Creg Baker
Source: Getty Images

Ya tabbatar da cewa Najeriya za ta yi amfani da tallafin yadda ya kamata tare da yin aiki da China wajen aiwatar da yarjejeniyoyin hadin gwiwar kasashen biyu.

Ya ce hakan zai kara karfafa zumunci tsakanin Najeriya da China tare da samar da karin alfanu ga al’ummomin kasashen biyu.

Najeriya da China sun sabunta yarjejeniya

Kun ji cewa gwamnatin Najeriya da Kasar China sun sabunta yarjejeniyar kudi wanda darajarta ta kai Yuan biliyan watau dala biliyan 2.

An yi wannan ne da nufin bunkasa kasuwanci da alakar da ke tsakanin Najeriya da ke Afrika ta yamma da kasar da ke Asiya.

Yarjejeniyar ta ba da damar a rika ciniki tsakanin kasashen biyu da kudin Naira da Yuan, wannan zai sa a huta da wahalar Dala.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262