Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Dakatar da Wasu Ciyamomin Kananan Hukumomi 3

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Dakatar da Wasu Ciyamomin Kananan Hukumomi 3

Kano - Rahotannin da muke samu yanzu na nuni da cewa majalisar dokokin jihar Kano ta dakatar da shugabannin kananan hukumomi uku.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

An ce majalisar ta dakatar da ciyamomin kananan hukumomin Bebeji, Rogo da Bagwai daga bakin aikinsu na tsawon watanni uku.

An dakatar da ciyamomi 3 a Kano

Mai magana da yawun majalisar dokokin jihar Kano, Kamaluddeen Sani Shawai ya tabbatar da hakan ga wakiliyar Legit Hausa ta wayar tarho a ranar 4 ga Agusta, 2026.

Kamaluddeen Shawai ya ce an yanke wannan hukunci ne a yayin zaman Majalisar, inda aka amince da dakatarwar domin ba da damar gudanar da bincike kan wasu batutuwan da suka shafi gudanar da ayyukansu.

Majalisar Kano ta ce matakin ya zama dole domin tabbatar da gaskiya, rikon amana da bin ka'idojin shugabanci a matakin kananan hukumomi.

"Majalisar dokokin jihar Kano ta dakatar da shugabannin kananan hukumomi guda uku, akwai Bebeji, akwai Bagwai akwai Rogo."

Kara karanta wannan

Wata cuta ta rage mugun iri, ta hallaka ƙasurgumin ɗan bindiga da ya addabi jama'a

- Kamaluddeen Sani Shawai.

Dalilin dakatar da ciyamomin Kano

Kamaluddeen Sani Shawai ya bayyana cewa:

"Kamar yadda aka sani akwai kwamitin da majalisar ta kafa kwanakin baya, wadanda suka zauna domin bibiyar korafe korafen da suka taso daga garuruwan yankunan da wasu kungiyoyi suka kawo a kan su shugabannin kananan hukumomin.
"Kwamitin ya zauna ya ci gaba da bibiyar lamura, kuma a yau sun gabatar da rahoto gaban majalisa, inda duk 'yan majalisar suka amince a dakatar da shugabannin na watanni uku.
"Wannan zai ba da damar a gudanar da bincike kan wadannan zarge zarge bisa adalci."

Zargen zargen da ake yi wa ciyamomi

Mai magana da yawun majalisar dokokin Kanon, ya yi karin haske da cewa ciyamomin da aka dakatar na iya rasa kujerunsu gaba daya idan har aka tabbatar da sun aikata zarge zargen da ake yi masu.

"

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com