Kananan hukumomin Najeriya
Majalisar dokokin jihar Osun ta dakatar da shugaban karamar hukumar Ede ta Kudu, Mr. Lukman Afolabi saboda furta kalaman cin mutunci ga kakakin majalisar jihar.
Babagana Zulum, gwamnan jihar Borno, ya umurci dukkanin ciyamomin kananan hukumomin jihar da su rinka sa hannu a na'urar shaidar zuwa aiki sau hudu a rana.
Gwamnatin Abba a jihar Kano ta fara rabon tallafin kayan abinci da suka hada da shinkafa ga ma'aikatan kananan hukumomi don rage radadin janye tallafin man fetur.
Akalla naira biliyan 1.95 gwamnatin jihar Zamfara ta ware don sake gina fadar sarakuna 18 da ke a fadin jihar, da nufin daga darajar masarautun gargajiya.
Wani mutum dan jihar Yobe, ya fara wani tattaki akan keke daga Damaturu zuwa jihar Delta don ganawa da Gwamna Sheriff Oborevwori, zai yi tafiyar kilo mita 1,200.
Jam'iyyar APC ta dakatarb da shugaban karamar hukumar Suleja da ke jihar Niger, Gambo Ibrahim kan zargin rashin ladabi da biyayya da kuma cin zarafin ofishinsa.
Majalisar dokokin jihar Kaduna ta dauki mataki kan wasu kansiloli guda takwas da suka tsige shugaban majalisar karamar hukumar Kagarko, dakatarwar ta din-din-din.
Olusegun Obansanjo, ya bayyana yadda ya ki ba INEC cin hanci a zaben kananan hukumomin jihar Ogun a shekarar 1998, lamarin da ya ja jam'iyyar PDP ta sha kaye.
Akalla mutane takwas ne suka mutu yayin da wasu da dama suka jikkata a wani hatsarin jirgin ruwa da ya rutsa da su a jihar Taraba. Gwamnan jihar ya magantu.
Kananan hukumomin Najeriya
Samu kari