Magana Ta Kare, An Shirya Mika Kudirin Kirkiro Yan Sandan Jihohi ga Shugaba Tinubu
- Kwamitin Shugaban Kasa kan Dokar Tsarin Aikin 'Yan Sanda ya ce zai mika kudirin ga Shugaban Kasa, Bola Tinubu ranar 3 ga Satumba, 2026
- Shugaban kwamitin kuma shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila, ya ce za a fara tattaunawa da masu ruwa da tsaki kafin a gabatar da kudirin
- Kwamitin ya bukaci 'yan Najeriya da kungiyoyi farren hula su gabatar da takardun shawarwarinsu a lokacin tattaunawa kan kudirin
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Kwamitin Shugaban Kasa kan Kudirin Dokar Tsarin Aikin 'Yan Sanda ya sanar da shirinsa na tattaunawa mai zurfi kafin mika kudirin ga shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu.
Kwamitin ya bayyana cewa zai gabatar wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu da kunshin kudirin dokar kirkiro rundunar yan sandan jihohi a ranar 3 ga watan Satumba, 2026.

Source: Twitter
Jaridar The Cable ta rahoto cewa shugaban kwamitin kuma Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Kasa, Rt. Hon. Femi Gbajabiamila, ne ya bayyana hakan yau Litinin, 3 ga watan Agusta, 2027.
Yayin da kwamitin yake wa manema labarai bayani kan halin da ake ciki a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja, Gbajabiamila ya ce za a bai wa yan Najeriya damar ba da shawarwari.
Matakin da za a dauka kafin a gabatar da kudirin
Femi Gbaj"abiamila ya bayyana cewa kafin a mika kudirin ga Shugaba Tinubu, za a gudanar da tattaunawa da masu ruwa da tsaki kan daftarin da aka tsara game da rundunar yan sandan jihohi.
Ya ce manufar hakan ita ce tabbatar da cewa an samu ra'ayoyi daga bangarori daban-daban kafin a dauki matakin karshe, kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito.
An bukaci jama'a su gabatar da shawarwari
Kwamitin ya kuma bukaci 'yan Najeriya, kungiyoyi masu zaman kansu da sauran masu ruwa da tsaki su gabatar da takardun shawarwari, bayanan matsayinsu da kuma hanyoyin da suke ganin za su taimaka wajen inganta kudirin.
A cewar Femi Gbajabiamila, shawarwarin za su bai wa jama'a damar nazarin ainihin tanade-tanaden kudirin, matakan kariya da aka tanada, tsarin samar da kudade da kuma yadda za a aiwatar da sauye-sauyen da dokar za ta kunsa.

Source: Twitter
Ya bayyana cewa 'yan Najeriya za su iya bayar da gudummawa da shawarwari kai tsaye wajen tsara dokar ta hanyar fura takardu ta shafin yanar gizo (nationalpolicingbill.com).
Majalisa shari'a ta ja hankali kan kudirin
A wani rahoton na daban, kun ji cewa Majalisar Koli ta Shari'ar Musulunci a Najeriya (SCSN) ta bada shawara kan gyaran kundin tsarin mulki game da kafa 'yan sandan jihohi.
A wata sanarwa da Sakatare Janar na majalisar, Nafiu Baba Ahmad, ya fitar, SCSN ta ce ta na bibiyar muhawarar da ake yi da kuma matakan da ake dauka kan batun kafa 'yan sandan jihohi.
Majalisar ta bukaci shugaban kasa, Majalisar tarayya da sauran masu ruwa da tsaki su kammala cikakkiyar tuntuba da 'yan Najeriya tare da magance damuwar jama'a kafin ci gaba aiwatar da kudirin.
Asali: Legit.ng

