Asirin Isra'ila Ya Tonu yayin da Ta Yi Yunkurin Kafa Gwamnati a Iran

Asirin Isra'ila Ya Tonu yayin da Ta Yi Yunkurin Kafa Gwamnati a Iran

  • Wani rahoto ya bayyana yadda Isra'ila ta yi shekaru tana ƙulla alaka da tsohon shugaban Iran Mahmoud Ahmadinejad a asirce
  • An ce sun yi tarurrukan sirri a Budapest a shekara 2024 da 2025, inda tsohon shugaban Mossad David Barnea ya hadu da shi
  • Rahoton ya nuna cewa shirin ya ci tura ne bayan jami'an IRGC sun gano zargin alaka tsakanin Ahmadinejad da Isra'ila

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Abuja - An fitar da wani rahoto mai ban mamaki ranar Litinin, inda ta nuna yadda hukumar leƙen asiri ta Isra'ila, Mossad, ta yi yunƙurin amfani da tsohon shugaban Iran Mahmoud Ahmadinejad a matsayin shugaban Iran.

A cewar rahoton, wannan ƙoƙari ya faro shekaru da dama kafin yaƙin Amurka da Isra'ila a kan Iran da ya ɓarke a farkon wannan shekarar.

Kara karanta wannan

Rashin sani: Shaguben da sanatan Amurka ya yi ga Iran kwana 5 kafin ya mutu

Mahmoud Ahmadinejad da Benjamin Netanyahu
Mahmoud Ahmadinejad a hagu da Benjamin Netanyahu a dama. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

New York Times ta ce hukumar Mossad ta ci gaba da tattaunawa a asirce da Ahmadinejad, har an shirya tarurruka a Budapest, babban birnin Hungary, a lokacin ziyarorin da Ahmadinejad ya yi a shekarun 2024 da 2025.

Rahoton ya ƙara nuna cewa tsohon shugaban Mossad David Barnea ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka hadu da Ahmadinejad a birnin Budapest.

Yadda asirin Isra'ila ya tonu

A ƙarshen watan Fabrairun 2025, lokacin da yaƙin tsakanin Isra'ila da Iran ya ɓarke, an zargi jami'an Mossad da yunƙurin fitar da Ahmadinejad daga birnin Tehran, a matsayin wani ɓangare na tsarin kawar da gwamnatin Khamenei.

Sai dai an kai a kan gidan Ahmadinejad kafin jami'an leƙen asiri su kai shi wani waje mai aminci a cikin kasar Iran. Daga bisani, Ahmadinejad ya bar wannan wuri a ɓoye, kuma ba a san takamaiman yadda hakan ya faru ba.

Rahoton i24 News ya nuna cewa Bayan ɓacewa na ɗan lokaci, Ahmadinejad ya sake bayyana a fili a makon da ya gabata, a lokacin jana'izar marigayi babban jagoran kasar Iran, Ali Khamenei.

Kara karanta wannan

Alaka ta munana: An hada baki da sojoji aka tsare dan majalisar Amurka a Isra'ila

Ahmadinejad yana ina a yanzu?

Jami'an Iran guda huɗu sun bayyana cewa yanzu ana zargin an sanya Ahmadinejad a kulle a gidansa, bayan hukumar leƙen asiri ta reshen sojin IRGC ta gano bayanan da ake zargi game da alaƙarsa da Isra'ila.

Jami'an Isra'ila sun ƙi yin sharhi kan rahoton, haka ma mai magana da yawun Ahmadinejad ya ƙi amsa tambayoyin da 'yan jaridar suka yi masa.

Mojtaba Khamenei a Iran
Jagoran kasar Iran, Mojtaba Khamenei. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Trump ya ce zai kwace Hormuz

A wani labarin, mun kawo muku cewa shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa yana shirin kwace ikon sarrafa mashigar ruwan Hormuz.

Hakan na zuwa ne yayin da ake cigaba da takun saka tsakanin kasashen Amurka da Iran bayan tsagaita wutar da suka yi a baya ta rushe.

A wata sanarwar da ya fitar, Trump ya bayyana cewa Amurka za ta cigaba da karbar haraji a mashigar Hormuz saboda kariya da za su bayar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng