Ginin Majalisar Gombe Ya Rufta kan Mutane, Gwamnati Ta Dauki Matakin Gaggawa
- Gwamnatin Gombe ta ba da umarnin gudanar da binciken gaggauta bayan ruftawar wani ɓangare na sabon ginin majalisar dokokin jihar
- Gwamna Inuwa Yahaya ya jajanta wa iyalan wanda ya rasu a iftila'in tare da cewa gwamnati za ta ɗauki nauyin jinyar wadanda suka jikkata
- An bai wa kamfanin ginin da masu kula da aikin wa'adin sa'o'i 24 su gabatar da cikakken rahoton musabbabin aukuwar lamarin
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Gwamnatin jihar Gombe ta ba da umarnin gaggauta gudanar da bincike kan ruftawar wani ɓangare na rumfar shiga sabon ginin Majalisar Dokokin Jihar Gombe da ake ginawa.
Lamarin, wanda ya faru a ranar Juma'a, ya yi sanadin mutuwar mutum ɗaya tare da jikkata ma'aikatan gini bakwai.
Gwamnati ta fara bincike domin gano musabbabin ruftawar wani ɓangare na rumfar shiga sabon ginin Majalisar Dokokin jihar Gombe
A cikin wata sanarwa da sakataren dindindin na Ma'aikatar Ayyuka, Gidaje da Sufuri, Danladi Adamu, ya fitar, gwamnatin ta ce sashen da ya rufta wani ɓangare ne na rumfar shiga ginin da ake ci gaba da ginawa.
Sanarwar ta ce ma'aikata biyar daga cikin waɗanda suka jikkata na karɓar magani a Asibitin Kwararru na Jihar Gombe, yayin da wasu biyu ke samun kulawa a Asibitin Koyarwa na Tarayya (FTH), Gombe.
Gwamna Inuwa Yahaya ya jajanta wa iyalan mamacin tare da ba da umarnin ɗaukar nauyin jinyar dukkan ma'aikatan da suka jikkata
Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa ga iyalan mutumin da ya rasu.
Ya kuma ba da umarnin cewa gwamnatin jihar za ta ɗauki nauyin kula da lafiyar dukkan ma'aikatan da suka jikkata har sai sun warke.
Bugu da ƙari, gwamnan ya umurci Ma'aikatar Ayyuka, Gidaje da Sufuri tare da hukumomin gaggawa, na sa ido da kuma ƙwararrun injiniyoyi su fara bincike domin gano musabbabin aukuwar lamarin.
Kamfanin ginin da masu kula da aikin sun samu wa'adin sa'o'i 24 su gabatar da rahoton abin da ya faru ga gwamnatin jihar
A matsayin wani ɓangare na binciken, gwamnatin ta umarci kamfanin da ke gudanar da aikin da kuma masu kula da shi su gabatar da cikakken rahoton abin da ya faru cikin sa'o'i 24.
Haka kuma, an buƙace su su gabatar da rahoton binciken farko, sannan daga baya su miƙa cikakken rahoton fasaha da zai ƙunshi sakamakon bincike da shawarwarin da suka dace.
Gwamnatin jihar ta ce sakamakon binciken ne zai jagoranci matakan da za ta ɗauka, tare da jaddada aniyarta na tabbatar da bin ƙa'idojin tsaro, inganci da ƙa'idodin aikin injiniya a dukkan ayyukan gine-ginen gwamnati.
Asali: Legit.ng

