'Ka Tuna Kamfen da Muka Yi Maka a Baya': Matar El Rufai Ta Roki Tinubu

'Ka Tuna Kamfen da Muka Yi Maka a Baya': Matar El Rufai Ta Roki Tinubu

  • Matar tsohon gwamnan Kaduna, Hajiya Asia El-Rufai, ta roƙi Shugaba Tinubu game da halin da mijinta ke ciki
  • Asia ta ce sun yi wa Tinubu kamfen sosai a zaɓen 2023, tana jaddada cewa ba sa neman tsoma baki, sai dai a ba El-Rufai beli mai sauƙi
  • Iyalan El-Rufai sun zargi ana hana shi likitocinsa, lauyoyinsa da 'yan uwansa, yayin da ICPC ke zargin ya karya sharuɗɗan ziyarar jinya a tsare.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Matar tsohon gwamnan Kaduna, Hajiya Asia El-Rufai ta roƙi Shugaba Bola Tinubu kan halin da Nasir El-Rufai ke ciki.

Asia ta bukaci Tinubu ya tabbatar mijinta ya samu adalci da haƙƙoƙin da kundin tsarin mulki ya tanada.

Asia ta yi wannan kira tare da matar El-Rufai ta biyu, Aichatou, a Abuja, tana mai cewa ba sa neman shugaban ƙasa ya tsoma baki, cewar Punch.

Kara karanta wannan

Matar Tinubu za ta tara matan Kano ta ba su tallafin kayan sana'a

Ta ce suna so kawai a bai wa tsohon gwamnan damar cin gajiyar haƙƙoƙin da doka ta bai wa duk wani ɗan Najeriya.

Kiran nata ya zo ne bayan ICPC ta tabbatar da kama likitan El-Rufai, Farfesa Bello Abubakar, bisa zargin yin bayanan ƙarya kan ziyarar jinyarsa.

Asia ta kuma yi zargin cewa mijinta na fama da hawan jini da ciwon sukari, amma ana hana shi samun kulawar lafiya yadda ya kamata.

Ta tunatar da irin rawar da ita da mijinta suka taka wajen yaƙin neman zaɓen Shugaba Tinubu a zaɓen shugaban ƙasa na 2023.

Ta ce:

"Ya Shugaba, na yi maka kamfen a ko'ina cikin Kaduna, mijina ya tsaya tare da kai. Shin wannan ne sakamakon?"

Asia ta ce komai na iya sauyawa idan Shugaba Tinubu ya ɗauki mataki, tana mai bayyana cewa suna ganin shugaban mutum ne mai tausayi.

Ta jaddada cewa ba sa neman a dakatar da shari'ar El-Rufai, amma suna son a mutunta haƙƙoƙinsa kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Ta ce a ba shi beli mai sauƙin cikawa, sannan kotu ta yanke hukunci idan an same shi da laifi ko kuma aka wanke shi.

Kara karanta wannan

Komai zai fito: APC na shirin fitar da bayanan mataimakin Tinubu a 2027

Asia ta yi zargin cewa ci gaba da tsare El-Rufai da hana shi ganin likitoci, lauyoyi da 'yan uwansa ya jefa iyalansu cikin tashin hankali.

Ta ce kullum suna rayuwa cikin fargabar samun mummunan labari, tana mai cewa abin da ake yi musu tamkar yaƙin ƙwaƙwalwa ne.

Ta kuma tambayi wanene ya bayar da umarnin hana Farfesa Bello Abubakar ganin kowa na tsawon sa'o'i ashirin da huɗu.

Iyalan sun ce ana hana El-Rufai damar ganin likitocinsa na kai tsaye, yayin da ziyarar 'yan uwa ta ƙara zama mai wahala.

Sun kuma nuna shakku kan rahoton lafiya da aka danganta da Asibitin Ƙasa da ke Abuja, suna neman a binciki sahihancinsa.

Asia ta ce waɗannan takunkumai sun hana El-Rufai samun isasshen lokaci da damar shirya kare kansa a gaban kotu.

Ta sake roƙon a ba shi beli cikin sharuɗɗan da zai iya cikawa har zuwa lokacin da za a kammala shari'arsa.

Ta ce ba sa gudun kare kansu a kotu, amma suna son a gudanar da shari'a cikin adalci da ba shi damar kare kansa.

A cewarta, El-Rufai ba zai iya shirya kariyarsa yadda ya kamata ba idan yana tsare kuma yana da ƙarancin damar ganin lauyoyinsa.

Kara karanta wannan

Gwamna Dauda Lawal ya tirje, ya yi magana kan sulhu da ƴan bindiga a Zamfara

ICPC ta bayyana cewa El-Rufai ya karya sharuɗɗan ziyarar jinya da kotu ta amince da ita yayin da yake tsare a hannunta.

Hukumar ta kuma ce ta kama likitansa, Farfesa Bello Abubakar, bisa zargin yin bayanan ƙarya dangane da lamarin.

ICPC ta ce ta sauƙaƙa ziyarar jinyar El-Rufai ne domin bin umarnin kotu da kuma mutunta haƙƙoƙin mutanen da ke tsare.

Hukumar ta ce Babbar Kotun Kaduna ta ware ranakun 6, 7 da 8 ga Yuli, 2026 domin ci gaba da sauraron shari'ar.

Sai dai ta ce El-Rufai bai halarci zaman farko ba, saboda ya dage sai ya fara ganin likitansa kafin a kai shi kotu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.