Mariya Bunkure: Ministar Tinubu Ta Kunyata 'Hadiminta' da Ya Yi Nade Naden Mukamai

Mariya Bunkure: Ministar Tinubu Ta Kunyata 'Hadiminta' da Ya Yi Nade Naden Mukamai

  • Karamar Ministar babban birnin tarayya Abuja, Mariya Mahmoud Bunkure, ta nesanta kanta daga wani mai ikirarin hadiminta ne
  • Dr. Mariya ta bayyana cewa mutumin wanda ya yi nade-naden mukamai a karkashin ofishinsa, ba ya aiki tare da ita
  • Karamar Ministar ta bukaci jama'a da kafafen yada labarai da su rika samun bayanan ayyukanta daga wuraren da suka dace

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Karamar Ministar Abuja Dr. Mariya Mahmoud, ta nesanta kanta daga wasu naɗe-naɗe da aka yi iƙirarin cewa Bin Usman Rano ne ya sanar da su.

Usman Rano dai ya gabatar da kansa a matsayin hadimin Ministar kan yaɗa labarai kuma ya ambaci sunayen masu ba da shawara guda bakwai a ƙarƙashin ofishinsa.

Mariya Mahmoud ta nesanta kanta da nade-nade
Karamar Ministar Abuja, Dr. Mariya Mahmoud a cikin ofis Hoto: Dr. Mariya Mahmoud
Source: Facebook

Ministar ta nesanta kanta ne a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin ta hannun mataimakinta na musamman kan yaɗa labarai, Austine Elemue, wanda aka sanya a shafinta na Facebook a ranar Litinin, 22 ga watan Yunin 2026.

Kara karanta wannan

An bukaci jihohi 26 su shirya saboda fargabar ambaliyar ruwa a 2026

Mariya Bunkure ta nesanta kanta da nade-nade

A cikin sanarwar, an bayyana naɗe-naɗen a matsayin waɗanda ba su da alaƙa da Ofishin karamar Ministar Abuja.

Elemue ya bayyana cewa shi ne kaɗai mataimaki na musamman kan yaɗa labarai da aka naɗa bisa ƙa'ida kuma yake da ikon fitar da sanarwa a hukumance a madadin Dr. Mariya Mahmoud.

Ministar ta ce ba hadiminta ba ne

A cewar sanarwar, Rano ba ya aiki a ofishin Ministar, a maimakon haka yana da alaƙa ne da ƙungiyar "Dr. Mariya Support Group," wata ƙungiyar siyasa da ke goyon bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Gwamna Abba Kabir Yusuf gabanin babban zaɓen 2027.

“Duk wani naɗi, muƙami, sanarwa ko izini da Usman Rano ya bayar, sun ta'allaka ne kaɗai da al'amuran ƙungiyar tallatawar kuma ba su da wata alaƙa ko kaɗan da ofishin mai girma karamar Ministar Abuja ko hukumar gudanarwar babban birnin tarayya Abuja (FCTA)."

- Austin Elemue

Kara karanta wannan

Andy Burnham: 'Dan siyasar da ake hasashen zai zama Firayim Ministan Birtaniya

An yi nadi da sunan Ministar Tinubu

An ruwaito cewa Usman Rano ya sanar da naɗin wasu mataimaka bakwai a ƙarshen mako, ciki har da masu ba da shawara kan yaɗa labarai, yarjejeniyar taro, al'amuran ɗalibai, matasa da wasanni, al'amuran addini, da kuma ayyuka na musamman.

Mariya Mahmoud ta nesanta da wani da ya ce hadiminta ne
Dr. Mariya Mahmoud na jawabi a wajen kaddamar da aiki a Abuja Hoto: Dr. Mariya Mahmoud
Source: Facebook

Ofishin Ministar ya buƙaci jama'a, ƙungiyoyin yaɗa labarai, da hukumomin gwamnati da su dogara ga hanyoyin sadarwa na hukuma kaɗai domin samun bayanai game da ayyukanta da ofishinta.

Sanarwar ta kuma sake jaddada sadaukarwar Ministar ga gaskiya, riƙon amana, da ingantacciyar sadarwa wajen sauke nauyin da ke kanta.

Tinubu ya yi wa Peter Obi martani

A wani labarin kuma, kun ji cewa Fadar shugaban kasa ta yi martani ga Peter Obi bayan ya bukaci Shugaba Bola Tinubu ya yi murabus.

Fadar shugaban kasan ta soki Peter Obi inda ta bayyana kiran murabus din da ya yi, a matsayin katsalandan ga dimojuradiyya.

Ta bayyana cewa kwatanta Tinubu da Keir Starmer, ya fallasa rashin fahimtar tsohon gwamnan na Anambra game da tsarin mulkin Najeriya.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng