Sarkin Musulmi Ya Yi Fatali da Jitar Shirin Maida Najeriya Kasar Musulunci

Sarkin Musulmi Ya Yi Fatali da Jitar Shirin Maida Najeriya Kasar Musulunci

  • Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa'ad Abubakar III ya musanta rade-radin cewa ana shirin musuluntar da Najeriya
  • Sultan ya jaddada cewa Musulmi ba su da wata manufa ta kawar da Kiristoci, yana mai cewa Allah cikinnhikimarsa ya hada addinan biyu a wuri daya
  • Sarkin ya kuma yi Allah-wadai da danganta laifukan ta’addanci da addini, yana mai cewa ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda ba su da alaka da musulmi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Sokoto, Nigeria - Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya (NSCIA), Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya karyata rade-radin cewa ana shirin musuluntar da Najeriya.

Mai Alfarma Sarkin Musulmin ya bayyana irin wannan magana a matsayin abin da ba zai yiwu ba, wanda aka kirkira da nufin raba kan al’umma.

Sarkin Musulmi.
Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar III a wurin taro Hoto: Daular Usmaniyya
Source: Getty Images

Ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a taron farko na Majalisar Tattaunawar Addinai ta Najeriya (NIREC) da aka gudanar a Abuja, kamar yadda Vanguard ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Bayan abin da ya faru, an haramta wa masu digirin girmamawa amfani da 'Dr' a Najeriya

Da gaske ana shirin musuluntar da Najeriya?

Sultan ya jaddada cewa Musulmi ba su da wata manufa ta kawar da Kiristoci, yana mai cewa Allah ne da hikimarsa ya hada addinan biyu domin wami dalili da ba wanda ya sami.

Sarkin, wanda shi ne shugaban haɗin gwiwa na NIREC, ya ce majalisar na ci gaba da zama muhimmin dandali na tattaunawa, wanda ya bayyana a matsayin hanya mafi dacewa don warware matsalolin ƙasa.

Ya kuma ce a tsawon shekaru 20 da ya yi a cikin majalisar, bai taba rasa halartar wani taro ba, abin da ya nuna jajircewarsa wajen tabbatar da zaman lafiya.

“Muna ganin tattaunawa da juna ta fi mu rika fada tsakaninmu, mu fahimci bambance-bambancenmu, sannan mu yi ƙoƙarin kawar da su; ni Musulmi ne, kai Kirista ne, dole mu zauna tare cikin girmamawa,” in ji shi.

Sarkin Musulmi ya gargadi malamai

Tribune Nigeria ta ruwaito cewa da yake magana kan batun fahimtar addini, Muhammad Sa'ad Abubakar ya yi gargadi kan karuwar malamai na bogi da ba su da zurfin ilimi a addini.

Kara karanta wannan

Baba Ahmed ya fadi 'babbar' matsalar da Musulunci ke fuskanta a karkashin Tinubu

Ya bayyana cewa iya harshen Larabci ba ya nufin mutum malamin Musulunci ne, kamar yadda ya ce akwai fastoci a wasu sassan Gabas ta Tsakiya da ke wa’azi da Larabci.

Ya bukaci shugabannin addinai su kasance masu ilimi sosai domin su jagoranci mabiyansu yadda ya kamata tare da hana amfani da addini wajen son zuciya ko manufofin siyasa.

NIREC.
Sarkin Musulmi, Muhammad Sa'ad Abubakar III a wurin taron farko na Majalisar NIREC Hoto: Daular Usmaniyya
Source: Facebook

Musulmai na da hannu a ta'addanci?

Sarkin ya kuma yi Allah-wadai da danganta laifuffukan ta’addanci da addini, yana mai cewa ya kamata a kira ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda da sunansu ba tare da alakanta su da Musulunci ba.

Ya jaddada cewa duk wanda ya kashe mutum mara laifi da sunan addini, “wuta ce makomarsa,” domin Musulunci ya dauki kashe mutum daya tamkar kashe dukkan bil’adama.

Sultan ya ja hankali kan matasa

A wani labarin, kun ji cewa Sarkin Musulmin ya nuna illar da ke tattare da yin watsi da matasa wadanda ke rayuwa a cikin al'umma ba tare da samar musu da abin dogaro da kai ba.

Ya ce zuba jari wajen ƙarfafa matasa ta hanyar koyon sana’o’i, kasuwanci da tsarin ba da jagoranci, na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da zaman lafiya.

Sarkin Musulmin ya bayyana cewa matasan da ba su da aiki kuma suke cikin takaici sun fi saurin faɗa wa cikin laifuffuka da sauran munanan ɗabi’u.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262