Shiriya daga Allah: Yadda Karamin Abu Ya Sa Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Ya Daina Shan Giya
- Farfesa Yemi Osinbajo ya bayyana yadda kalaman wani mutumi a kasar Somaliya suka jawo ya daina shan giya gaba daya
- Tsohon mataimakin shugaban kasar ya ce duk da kasancewarsa Fasto, yana shan giy amma daga baya ya daina harka da barasa
- Oainbajo ya rike kujerar mataimakin shugaban kasa a tsakanin 2015 zuwa 2023 lokacin mulkin Marigayi Muhammadu Buhari
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Farfesa Yemi Osinbajo, ya bada labarin yadda wani lamari da bai taka kara ya karya ba, ya sa ya daina shan giya gaba ɗaya.
Farfesa Osinbajo ya ce duk da kasancewarsa malamin coci, yana shan giya musamman wacce ake kira da 'jar giya' lokaci zuwa lokaci.

Source: Getty Images
A rahoton da jaridar Punch ta tattaro, tsohon mataimakin shugaban kasar ya ce daga baya ya daina shan giya gaba daya.
“Na kan sha jar giyar inabi wani lokaci, haka kuma ina son giya,” in ji shi
Sai dai ya ce wani abu da ya faru a birnin Mogadishu da ke kasar Somaliya, lokacin da yake aiki da Majalisar Dinkin Duniya ya canja masa ra’ayi har ta kai ga ya daina shan giya.
Maganar da ta sa Osinbajo ya daina shan giya
Ya ce wata rana Lahadi bayan ya yi wa’azi a taron ibada, yana hanyarsa ta zuwa siyan kwalaben giya biyu domin komawa daki ya karanta Littafi Mai Tsarki.
Osinbajo ya ce da ya shiga wani gidan cin abinci a cikin unguwar da gidajen ma'aikatan Majalisar dinkin duniya suke, ya tarar da abokan aikinsa daga kasashe daban-daban suna shan giya.
A cewarsa, da suka gan shi, sai suka ɓoye giyarsu, yayin da ya tambayi wani abokinsa dan ƙasar Denmark dalilin da ya sa ya ɓoye giya, sai ya ce masa:
“Kai fasto ne, ba za mu iya shan giya a gabanka ba."
Darasin da Farfesa Osinbajo ya dauka

Kara karanta wannan
Mutanen jihar Kano na cikin alheri a mulkin Tinubu, an raba wa talakawa Naira biliyan 48
Farfesa Osinbajo ya ce wannan lamari ya zama masa kamar saƙo daga Allah, wanda ya sa ya fahimci ma’anar cewa komai na iya halatta ga bil'adama amma ba duka suke da amfani ba.
Ya ce tun daga wannan rana da mutumin ya gaya masa wannan magana, bai ƙara shan giya ba, cewar rahoton Vanguard.

Source: Twitter
Yemi Osinbajo ya ba da wannan labari ne a wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta.
Bidiyon ya jawo cece-kuce a kafafen sada zumunta, inda wasu suka ga labarin a matsayin abin dariya kuma mai ma’ana, yayin da wasu suka yi amfani da damar wajen tattauna rayuwarsa da rawar da ya taka a siyasa.
Osinbajo ya nemi matasa su shiga siyasa
A wani labarin, kun ji cewa Farfesa Yemi Osinbajo ya buƙaci ƴan Najeriya, da su rika shiga harkokin siyasa domin amfani da ita a matsayin hanyar samar da shugabanci nagari.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasan ya nuna cewa duk da mummunan suna da siyasa ke da ita a halin yanzu, ita ce kaɗai hanyar gyara kasa ta kafa jagoranci nagari.
Yayin da yake magana kan matasan Najeriya da ke da burin shiga ofisoshin gwamnati, ya nuna cewa wajibi ne su kasance cikin shiri ta fuskar ilimi tare da fahimtar yadda shugabanci ke aiki.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng
