Za a Gurfanar da Sojoji 36 da Ake Zargi da Yunkurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki gaban Kotu

Za a Gurfanar da Sojoji 36 da Ake Zargi da Yunkurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki gaban Kotu

  • A shekarar da ta gabata hukumomin tsaro suka cafke wasu sojoji bisa zargin yunkurin kifar da gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu
  • Hedkwatar tsaro ta kasa ta shirya gurfanar da wadanda ake zargi a gaban babbar kotun soja domin yi masu shari'a
  • An bayyana cewa za a ba su damar daukar lauyan da zai kare su kan tuhume-tuhumen da za a shigar a kansu

​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Aƙalla jami'an sojoji 36 waɗanda ake zargi da yunkurin juyin mulki ga Shugaba Bola Tinubu ne za a gurfanar a gaban kotu.

Za a gurfanar da jami'an ne a gaban babbar kotun soja (GCM) ranar Juma'a, 24 ga watan Afirilun 2026, biyo bayan kafa kwamitin shari'ar soja da hedkwatar tsaro ta yi.

Za a gurfanar da sojojin da suka yi yunkurin kifar da Tinubu gaban kotu
Babban hafsan hafsoshi, Janar Olufemi Oluyede da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu Hoto: Dauda Lawal, Bayo Onanuga
Source: Facebook

Kodayake hedkwatar tsaro ba ta sanar da matakin a bayyane ba, jaridar Sahara Reporters ta fitar da rahoton.

Kara karanta wannan

Kotu ta soke belin tsohon hadimin El Rufai, an kara ingiza keyarsa zuwa kurkuku

Za a fara zaman kotu don shari'ar sojoji

An bayyana cewa kotun ta GCM za ta taru a Scorpion Officers’ Mess, Asokoro, Abuja ranar 23 ga Afrilu, a cewar umarnin kiran taron da AM Alechenu, kwamandan rundunar hedkwatar tsaro, ya sanya wa hannu.

Umarnin, mai kwanan wata 17 ga Afrilu, ya nuna cewa 'yan sandan soja, na ruwa, da na sama tare da dakarun Guards Brigade ne za su tsare wurin, yana mai ƙarawa da cewa ba a amince wa kowa ya kawo makami cikin zauren kotun ba.

Masu tsaron kotun ne kawai aka amince masu su “ɗauki makamai a kewayen harabar kotun a duk ranar da ake gudanar da shari'a.”

A cewar umarnin, an kafa kwamitin ne kamar yadda dokar rundunonin soja ta dokokin tarayyar Najeriya ta 2004 ta tanada.

Ana zargin sojoji da yunkurin kifar da Tinubu

Jaridar Premium Times ta ce waɗanda za a gurfanar ɗin suna cikin babban rukunin jami'an da ake tsare da su tun shekarar 2025 sakamakon zargin yunkurin juyin mulki.

Kara karanta wannan

Kotu ta dauki matakin farko kan wadanda ake zargi da yunkurin yi wa Tinubu juyin mulki

Kwamitin yana ƙarƙashin jagorancin Air Vice Marshal H.I. Alhaji a matsayin Shugaba, tare da mambobi da suka haɗa da Manjo Janar-Janar UT Opuene, IB Abubakar, NUC Ogili, SA Emmanuel da FU Mijinyawa.

Sauran sun hada da Rear Admiral D.M. Ndanusa da Rear Admiral MK Igwe; da kuma Air Vice Marshals M.A. Isah da A.O. Kotun. Air Vice Marshal M.M. Omar yana matsayin mamban jiran ko ta kwana.

Umarnin ya nuna cewa za a gudanar da shari’ar ne a ƙarƙashin ikon da dokar rundunonin soja ta bayar. Ya kuma buƙaci cewa, da zarar an kammala shari’ar, dole ne shugaban kotun GCM ya tura bayanai kan zaman a cikin ƙayyadadden lokaci.

Za a gurfanar da sojoji gaban kotu
Babban hafsan hafsoshin Najeriya, Janar Olufemi Oluyede Hoto: @HQNigerianArmy
Source: Twitter

Wadanne tuhume-tuhume ake yi wa sojojin?

Kodayake umarnin kiran taron bai fayyace takamaiman tuhume-tuhumen dalla-dalla ba, ya nuna cewa “za a miƙa tuhume-tuhumen ga waɗanda ake zargin ɗaya bayan ɗaya.”

Bugu da ƙari, umarnin ya tabbatar da cewa duka masu ƙara da masu kariya za a ba su damar gabatar da shaidu daidai da tanadin dokar ba da shaida ta 2023.

Ya kuma tabbatar wa waɗanda ake zargin damar samun wakilcin lauyan da suka zaɓa, idan kuma ba su da lauya, za a samar masu da shi kyauta.

Kara karanta wannan

Kurunkus: An gurfanar da mutane 6 da ake zargi da yunkurin yi wa Tinubu juyin mulki a Najeriya

An gurfanar da masu yunkurin kifar da Tinubu

A wani labarin kuma, kun ji cewa Gwamnatin tarayya ta gurfanar da mutane shida kan zargin yunkurin juyin mulki ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu a gaban kotu.

An gurfanar da wadanda ake zargin ne kan tuhume-tuhume guda 13 da suka shafi zargin ta’addanci da cin amanar kasa.

Gurfanar da mutanen na zuwa ne bayan tsawon lokacin da aka shafe ana bincike kan zargin wasu jami'an sojojin Najeirya da fararen hula da kitsa yadda za a kifar da Shugaba Tinubu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng