Matawalle Ya Kai Tallafin N5m Gidan Limamin da 'Yan Bindiga Suka Kashe a Zamfara

Matawalle Ya Kai Tallafin N5m Gidan Limamin da 'Yan Bindiga Suka Kashe a Zamfara

  • Bello Matawalle ya jajanta wa iyalan Limamin Maru da aka kashe, ya ba da tallafin N5m da buhunan shinkafa da kayan abinci
  • An kashe limamin da wasu ’ya’yansa biyu bayan sace su da ’yan bindiga masu garkuwa suka yi a cikin watan azumi a jihar Zamfara
  • Ministan tsaron ya sha alwashin ƙara ɗaukar matakai domin kawo karshen ’yan bindiga a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Zamfara - Ministan tsaro, Bello Matawalle, ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayi Limamin Babban Masallacin Juma’a na Maru, Alkali Salihu Sulaiman.

Rahotanni sun tabbatar da cewa ’yan bindiga sun kashe limamin tare da ’ya’yansa biyu bayan garkuwa da su.

Matawalle
Matawalle ya ba da tallafin kudi ga iyalan limamin da aka kashe a Maru. Hoto: Zagazola Makama|Bello Matawalle
Asali: Facebook

Punch ta wallafa cewa Bello Matawalle ya ba da tallafin Naira miliyan 5, buhun shinkafa 10 da kuma sauran kayan abinci ga iyalan mamacin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanarwar da Sakataren Yaɗa Labarai na jam’iyyar APC ta jihar Zamfara, Malam Yusuf Idris ya fitar ta tabbatar da cewa wakilan Matawalle ne suka kai ziyarar.

Malam Yusuf Idris ya bayyana cewa an kai ziyarar ne karkashin jagorancin Sakataren APC na jiha, Ibrahim Dangaladima.

Matawalle ya yi addu’a da alƙawarin ƙarin tsaro

Matawalle ya roƙi Allah ya gafarta wa marigayin tare da ba iyalan sa da al’ummar Maru da masarautar Maru haƙurin jure rashin da suka yi.

Ya kuma nuna damuwa kan yadda barayin daji ke kara tsananta farmaki musamman ga malamai da shugabannin addini a jihar Zamfara.

Daily Nigerian ta rahoto cewa ministan ya ce ma’aikatarsa za ta ci gaba da tura karin jami’an tsaro zuwa Zamfara domin kawar da barayin daji gaba ɗaya.

Ya ƙara da cewa gwamnatin Bola Tinubu na ɗaukar matakai wajen ganin an dakile matsalar ta tsaro a Arewa maso Yamma.

Gwamnatin Tinubu na kokarin kawo zaman lafiya

Matawalle ya bayyana cewa shugaban ƙasa ya samar da dukkan kayan aiki da sojoji ke buƙata, tare da yin alƙawarin cewa nan ba da jimawa ba, za a dawo da zaman lafiya a yankin.

Ya bukaci jama’a su taimaka wa jami’an tsaro da sahihan bayanan leƙen asiri domin cimma nasara a yaki da ta’addanci.

Ya jaddada bukatar haɗin gwiwa tsakanin jihohin Arewa maso Yamma da gwamnatin tarayya don murƙushe ayyukan ta’addanci.

Salihu Sulaiman
Sarki Maru ya yi godiya ga Matawalle kan ta'aziyyar Alkali Salihu Sulaiman. Hoto: Zagazola Makama
Asali: Facebook

Sarkin Maru, Alhaji Abubakar Gado-Maigari, ya yaba da ziyarar da Matawalle ya aiko da ita, yana mai cewa hakan ya rage raɗaɗin da iyalan mamacin da al’ummar masarautar ke ciki.

An kama masu garkuwa bayan kisa a Kano

A wani rahoton, kun ji cewa gwamnatin Kano ta sanar da cafke wasu mutane biyar da suka yi garkuwa da wata yarinya 'yar shekara guda.

Abba Kabir Yusuf ya jinjina wa jami'an hukumar DSS bisa kokarin da suka yi na bin diddigin masu garkuwar.

Rahotanni sun tabbatar da cewa masu garkuwar sun kashe yarinyar kuma suka wurga gawarta cikin rijiya duk da karbar kudin fansa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng