'Farashin Abinci da Fetur Ya Sauka a Najeriya': Minista Ya Zayyano Alheran Tinubu

'Farashin Abinci da Fetur Ya Sauka a Najeriya': Minista Ya Zayyano Alheran Tinubu

  • Ministan sadarwa, Mohammed Idris, ya ce sauye-sauyen da shugaba Bola Tinubu ke aiwatarwa sun fara haifar da ɗa mai ido a Najeriya
  • Ya ce ana samun raguwar wahalhalu bayan aiwatar da manufofin gwamnati, ciki har da saukar farashin kayan abinci da na man fetur
  • Ministan ya bukaci shugabannin addini su yi addu’o’i tare da fahimtar da mabiyansu a muhimancin zaman lafiya da ci gaba

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Ministan sadarwa da wayar da kan 'yan kasa, Mohammed Idris, ya ba da tabbacin cewa tarihi zai yi wa shugaba Bola Tinubu adalci, duba da jajircewarsa wajen cigaban Najeriya.

A cewar ministan, Tinubu yana tafiyar da mulkinsa da kishin kasa da kuma cikakken tunani na sauke nauyin da Allah ya dora masa.

Kara karanta wannan

Ministocin Tinubu sun hada kai, ana shirin samawa matasa miliyan 5 aiki

Gwamnatin tarayya ta yi magana tasirin manufofin Shugaba Bola Tinubu
Minista ya ce manufofin Tinubu sun kawo sauyi mai kyau a Najeriya. Hoto: @officialABAT
Asali: Twitter

Idris ya bayyana hakan ne yayin taron manema labarai na ministoci da aka gudanar a Abuja, a ranar Alhamis, 13 ga Maris, inji rahoton Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An samu saukin farashin abinci da fetur

Mohammed Idris ya ce sauye-sauyen da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa suna da matukar muhimmanci wajen daidaita kasar a dogon zango.

Ya ce, duk da cewa matakan suna da wahala a yanzu, alamu na nuna cewa sun fara haifar da sakamako mai kyau a fannoni da dama.

"Mun tsallake mawuyacin hali, kuma wahalhalun da ke tattare da sauye-sauyen suna raguwa yayin da sakamakon ke fara bayyana," in ji shi.

Ministan ya kara da cewa, yanzu ana samun raguwar farashin abinci, daidaiton darajar Naira a kasuwar musaya, da saukar farashin man fetur, wanda ke nuna ingancin manufofin gwamnati.

'A kara hakuri' - Ministan sadarwa

Ya amince da cewa sauye-sauye masu muhimmanci sau da yawa suna fuskantar adawa saboda wahalhalun da ke tattare da su, amma ya jaddada cewa suna da matukar amfani ga cigaban kasa.

Kara karanta wannan

Ramadan: Gwamnan Jigawa ya kai ziyara wajen raba abinci, ya gano abin mamaki

"A duk duniya, tarihi ya nuna cewa duk wani sauyi mai ma’ana yana bukatar hakuri, sadaukarwa, da hangen nesa domin samun cigaba mai dorewa," in ji ministan.

Ya bayyana cewa wahalhalun da ake fuskanta a halin yanzu wata sadaukarwa ce da 'yan kasa za su yi domin samun ingantacciyar makoma ta tsawon lokaci.

Gwamnati ta sake tausasar zuciyar 'yan Najeriya

Ministan Ilimi, Mohammed Idris ya yi magana kan tasirin manufofin Tinubu
Ministan Ilimi, Mohammed Idris ya magantu kan tasirin manufofin Tinubu. Hoto: @HMMohammedIdris
Asali: Twitter

Idris ya gode wa ‘yan Najeriya bisa hakuri da goyon bayan da suke bai wa gwamnati, yana mai kira ga shugabannin addini da su ci gaba da yin addu’a domin zaman lafiya da tsaron kasa.

"Ina kira ga malamai Musulmi da Kiristoci su yi amfani da lokutan Ramadan da Azumin Lent wajen addu’o’i ga zaman lafiya da cigaban Najeriya,"

- in ji Idris.

A taron, ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, da ministan ilimi, Dr. Tunji Alausa, sun bayyana nasarorin da ma’aikatunsu suka samu a kokarin gwamnatin Tinubu na kawo ci gaba a kasar.

Kara karanta wannan

Tinubu zai nada mukamai, za a tura Jakadu a kasashen waje bayan watanni 18

Sun jaddada cewa gwamnatin na aiki tukuru don tabbatar da cewa manufofinta sun inganta rayuwar ‘yan Najeriya ta hanyar daukar matakan da suka dace domin cigaban kasa.

Farashin fetur zai ci gaba da sauka

A wani labarin, mun ruwaito cewa, masanin tattalin arziki, Bismarck Rewane, ya bayyana cewa farashin man fetur zai ci gaba da raguwa har zuwa Yuni 2025.

Ya yi wannan bayani ne bayan rage farashin fetur da kamfanin Dangote da NNPCL suka yi, wanda zai saukaka wa ‘yan Najeriya wahalhalu.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.