Alau: Gwamnatin Tinubu Ta Amince da Aikin N80bn a Borno, Ta Fadi Lokacin Farawa

Alau: Gwamnatin Tinubu Ta Amince da Aikin N80bn a Borno, Ta Fadi Lokacin Farawa

  • Gwamnatin tarayya ƙarƙashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu ta waiwayi aikin gyara madatsar ruwa ta Alau a jihar Borno
  • A yayin zaman majalisar zartarwa ta tarayya (FEC) da Bola Tinubu ya shugabanta, an amince da N80bn domin gudanar da aikin
  • Ministan albarkatun ruwa da tsaftar muhalli, Joseph Utsev, ya bayyana cewa za a kammala aikin a cikin watanni 24

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Majalisar zartarwa ta tarayya (FEC) ta amince da Naira biliyan 80 don sake ginawa da gyara madatsar ruwa ta Alau a jihar Borno.

A shekarar da ta gabata ne dai madatsar ruwan ta Alau ta ɓalle, wanda hakan ya jawo mummunar ambaliyar ruwa a birnin Maiduguri da wasu garuruwan.

Bola Tinubu ya amince a gyara madatsar ruwan Alau
Gwamnatin Tinubu za ta gyara madatsar ruwan Alau a Borno Hoto: @DOlusegun
Asali: Facebook

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da hadimin shugaba Bola Tinubu, Dada Olusegun, ya sanya a shafinsa na X.

Kara karanta wannan

Bayan ta karɓi Sanata daga PDP, jam'iyyar APC ta ƙara yin babban kamu a Najeriya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnatin Tinubu za ta gyara madatsar ruwan Alau

Ministan albarkatun ruwa da tsaftar muhalli, Joseph Utsev ya bayyana amincewar a ƙarshen taron FEC da Shugaba Bola Tinubu ya jagoranta a ranar Talata a fadar shugaban ƙasa.

Joseph Utsev ya ce gwamnatin jihar Borno ta yi haɗin gwiwa da gwamnatin tarayya don fara aikin, wanda za a kammala cikin watanni 24 masu zuwa.

Ya ƙara da cewa, aikin gyaran farko na madatsar ruwan zai gudana a tsakanin watan Fabrairu da Yuli domin tabbatar da cewa ba a samu ambaliyar ruwa a jihar ba a wannan shekarar.

“Na bayar da rahoto kan kwamitin da aka kafa a ranar 23 ga Satumba 2024 kan tantance madatsun ruwa a Najeriya. An ƙaddamar da kwamitin a ranar 2 ga watan Oktoba 2024."
“Shugaban ƙasa ya amince da Naira biliyan 80 don sake ginawa da gyara madatsar ruwa ta Alau a jihar Borno, kuma wannan yana jiran amincewar FEC yayin da ake bin dukkanin hanyoyin da suka dace."

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya ki amincewa da kafa sabuwar jami'a a Arewa, ya fadi dalili

"Ana aiki tare da gwamnatin jihar Borno don fara aikin tsakanin yanzu da watan Yuli 2025. Za a fara da sashi na farko don tabbatar da cewa ambaliya ba ta faru ba a jihar Borno a cikin 2025, aikin zai kammala cikin watanni 24 masu zuwa."

- Joseph Utsev

Gwamnati ta ɗauki mataki bayan ambaliya

A ranar 9 ga watan Satumba 2024, fiye da mutane 30 ne suka mutu sannan mutum 400,000 suka rasa matsuguni sakamakon ambaliya a Maiduguri, jihar Borno, saboda ɓallewar madatsar ruwa ta Alau, cewar rahoton TheCable.

Bayan ɓallewar madatsar ruwan, gwamnatin tarayya ta kafa kwamitin tantance lafiyar dukkanin madatsun ruwa a ƙasar, ciki har da Alau.

Kwamitin, wanda Joseph Utsev ke jagoranta, ya bayyana cewa sun ɗauki madatsar ruwan Alau a matsayin ta farko mafi muhimmanci da ya kamata a sake ginawa bisa ga tantancewar da suka yi.

Tinubu ya ƙi amincewa da kafa jami'a

A wani labarin kuma, kun ji cewa Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙi rattaɓa hannu kan dokar da za ta kafa jami'ar ilmi ta tarayya a jihar Adamawa.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya shiga ganawa da ministoci da manyan kusoshin gwamnati a Abuja

Shugaban ƙasan ya bayyana cewa akwai kura-kurai a cikin dokar, wanda hakan ne ya sanya ya ƙi amincewa da ita.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng