Shugaba Tinubu Ya Shiga Ganawa da Ministoci da Manyan Ƙusoshin Gwamnati a Abuja

Shugaba Tinubu Ya Shiga Ganawa da Ministoci da Manyan Ƙusoshin Gwamnati a Abuja

  • Shugaba Bola Tinubu yana jagorantar zaman FEC a Abuja don duba muhimman takardu bayan zaman farko na majalisar a 2025
  • Majalisar ta amince da Naira biliyan 4.8 don samar da fakitin maganin cutar kanjamau guda 150,000 daga Fabrairu zuwa Mayu 2025
  • Mataimakin shugaba, Sanata Kashim Shettima, shugaban ma'aikatan Aso Villa, Femi Gbajabiamila da ministoci sun halarci taron

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Shugaba Bola Ahmed Tinubu yana jagorantar zaman majalisar zartarwa ta tarayya (FEC) a fadar gwamnati da ke Abuja.

Wannan zama na yanzu ya biyo bayan taron majalisar na farko a shekarar 2025 wanda aka fara gudanar da shi a jiya Litinin.

Ministan watsa labarai ya yi magana yayin da Tinubu ke jagorantar taron majalisar FEC
Bola Tinubu ya shiga taron FEC a fadar shugaban kasa. Hoto: @aonanuga1956
Asali: Facebook

Tinubu ya jagoranci taron majalisar FEC

Rahoton The Nation ya nuna cewa an fara zaman majalisar FEC din ne da ƙarfe 1:26 na rana bayan isowar Bola Tinubu cikin ɗakin taron majalisar.

Kara karanta wannan

Bayan shawarar gwamnoni, majalisa za ta zauna domin tabbatar da kudirin haraji da gaggawa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ministan watsa labarai da wayar da kan al’umma, Mohammed Idris, ya sanar da manema labarai cewa taron majalisar zai kasance na kwana biyu.

A jiya Litinin, Mohammed Idris ya ce:

“Zaman majalisar zai ci gaba gobe saboda akwai muhimman takardu masu yawa da suka taru tun watan Disamba da ake son duba su."

Kusoshin gwamnati da suka halarci taron

Ministan ya ci gaba da cewa:

“Shugaban ƙasa ya na son a kammala duba dukkanin takardun don ci gaba da aiwatar da ayyukan gwamnati yadda ya kamata."

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, sakataren gwamnatin tarayya, George Akume, da shugabar ma’aikatan gwamnati, Didi Walson-Jack sun halarci taron.

Haka zalika, mahalarta taron sun hada da shugaban mma’aikatan fadar gwamnati, Femi Gbajabiamila da ministoci daban-daban na tarayya.

Gwamnati za ta kashe N4.5bn kan maganin HIV

A wani labarin, mun ruwaito cewa, majalisar zartarwa ta tarayya ta amince a kashe N4.5bn domin sayen magungunan cutar HIV har fatiki 150,000.

Kara karanta wannan

'Za mu iya': Tinubu ya dauki mataki da Amurka ta janye tallafin yaki da cutar HIV

Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Ali Pate, ya bayyana cewa kudurin ya biyo bayan tattaunawa kan tasirin sauye-sauyen manufofin Amurka.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.