An Koma Ruwa: Hatsabibin Dan Bindiga da Aka Sako daga Nijar Ya Dawo Katsina

An Koma Ruwa: Hatsabibin Dan Bindiga da Aka Sako daga Nijar Ya Dawo Katsina

  • Jagoran ‘yan bindiga Bammi Yarma ya dawo Najeriya bayan fitowa daga gidan yari a Nijar, bayan zaman kurkuku na shekaru tara
  • Bayyanarsa ya jefa fargaba a jihohin Katsina, Zamfara da Sakkwato, ganin yadda yake da tasiri tsakanin shugabannin ‘yan bindiga
  • Rahotanni sun ce manyan shugabannin ‘yan bindiga sun ba shi bindigogi masu yawa, wanda hakan na iya ƙara yawan hare-hare

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Katsina - Fitaccen shugaban ‘yan bindiga, Kachallah Bammi Yarma, wanda aka tsare a Jamhuriyar Nijar tun 2015, ya fito bayan cika wa’adin daurin shi.

Bammi Yarma, wanda aka fi sani da jagoran shugabannin ‘yan bindiga, ya dawo yankin Arewa maso Yamma, musamman jihar Katsina, bayan shekaru tara.

An gano cewa hatsabibin dan bindiga Kachallah Bammi Yarma ya koma ta'addanci a Arewa maso Yamma.
Hatsabibin dan bindiga, Kachalla Bammi ya fito daga gidan yarin Nijar, ya koma Arewa maso Yamma.
Asali: Original

Hatsabibin dan bindiga ya fito daga kurkuku

Zagazola Makama ya wallafa a shafinsa na X cewa an cafke Bammi Yarma a 2015 a lokacin mulkin tsohon gwamnan Katsina, Aminu Bello Masari, yayin da yake safarar makamai da raƙuma tara.

Kara karanta wannan

Sheikh Jingir ya fara gyara hanyar Saminaka da ta hada jihohin Arewa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A lokacin da aka kama shi, an kwace dabbobi fiye da 1,000 daga hannun ƙungiyarsa, wanda hakan ya katse musu babbar hanyar samun kayayyaki.

An gurfanar da shi kuma aka yanke masa hukunci a Jamhuriyar Nijar, inda ya yi zaman gidan yari na tsawon shekaru tara.

Dan bindigar ya fara jagorantar hare-hare

Rahotanni sun ce Bammi Yarma ya sake bayyana a yankin Arewa maso Yamma, inda ya jagoranci hare-hare da garkuwa da mutane da satar shanu.

Bayyanarsa ya je mutane cikin fargaba, ganin irin tasirin da yake da shi a tsakanin shugabannin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, da Sakkwato.

Rahotanni sun ce wasu manyan shugabannin ‘yan bindiga suna girmama shi, har suna ba shi makamai masu yawa, ciki har da bindigogi biyar zuwa goma.

Ana fargabar karuwar ta'addanci a Arewacin Najeriya

Masu nazari kan tsaro na ganin bayyanarsa na iya haifar da ƙaruwar hare-hare da tashin hankali a yankin Arewa maso Yamma.

Kara karanta wannan

Yayin da ake shirin zaben gwamna, an fadi shirin APC domin kwace mulki cikin sauki

Bammi Yarma ba kawai yana gudanar da ta’addanci ba ne, har ma ya na kashe wasu manyan shugabannin ‘yan bindiga, ciki har da Kachallah Kundu.

Ana tsoron cewa dawowarsa na iya tayar da sababbin rikice-rikicen ƙungiyoyin ‘yan bindiga ko ƙarfafa hare-haren da ake kai wa al’ummomi.

Sunan Bammi Yarma ya wuce iyakar Najeriya, har wasu ƙungiyoyin ta’addanci a Nijar da yankin Sahel na tsoron tasirinsa.

Katsina: 'Yan bindiga sun farmaki gidan ciyaman

A wani labarin, mun ruwaito cewa, wasu ƴan bindiga dauke da manyan makamai sun kai hari a gidan shugaban ƙaramar hukumar Malumfashi, jihar Katsina.

A yayin wannan mummunan farmakin, ƴan bindigan sun kashe wani jami’in ƴan sanda da ke tsaron gidan shugaban ƙaramar hukumar.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.