Rarara, Tijjani Gwandu da Taurarin da Suka Yi Nasarar Tallata ‘Yan Takara a Siyasa

Rarara, Tijjani Gwandu da Taurarin da Suka Yi Nasarar Tallata ‘Yan Takara a Siyasa

Abuja - Bayan dawowar siyasa a shekarar 1998, wakoki sun rika tasiri sosai wajen lashe zabe da samun kujerar mulki a Najeriya.

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.

Wakoki har a duniyar nan tana jawo hankalin masu yin zabe, ‘yan siyasar Arewacin Najeriya suna amfani da mawaka a yakin zabe.

Legit ta duba, ta zakulo wasu fitattun wakoki da shahararrun mawaka suka rera, wadanda ake ganin sun taimaka wajen lashe zabe.

wakokin siyasa
An yiwa Buhari da Abba wakokin siyasa a Najeriya Hoto: Abba Kabir Yusuf/Buhari Sallau
Asali: Facebook

Fitattun wakokin siyasa a Najeriya

1. 'Wakar Yau Najeriya riko sai mai gaskiya, Baba Buhari kai mu ke so Najeriya'

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shekaru 20 da suka wuce Ibrahim Yala ya rera wakar ‘Yau Najeriya riko sai mai gaskiya, Baba Buhari kai mu ke so Najeriya’.

Kara karanta wannan

Albashin Shugaban kasa, Ministoci da ‘Yan Majalisa shekaru 45 da suka wuce

Wannan waka ta taimaka wajen tallata Muhammadu Buhari a lokacin yana adawa da PDP, duk da a lokacin bai lashe zabe ba.

2. Wakar Dawo dawo

Nazifi Asnanic ya yiwa Rabiu Musa Kwankwaso wakar ‘Dawo dawo’ wanda ta yi tashe a 2011 da PDP ta sake karbe mulkin Kano.

Wakar ta nuna Kanawa sun yi kewar Kwankwaso shekaru takwas bayan Ibrahim Shekarau ya doke shi a karkashin jam’iyyar ANPP.

3. Masu gudu da su gudu

Wakokin da Dauda Kahutu Rarara ya yi a lokacin zaben 2015 sun ba da gudumuwa wajen ganin bayan Goodluck Jonathan da PDP.

Rarara ya yi wakoki irinsu ‘Masu gudu su gudu’ da ‘mai malfa karya ta kure’ a lokacin daga baya mawakin ya juyawa gwarzonsa baya.

4. Abba Gida Gida, Abba

Abba Kabir Yusuf ya kara samun shahara a siyasa ne saboda wakar Abba Gida Gida, Abba wanda Tijjani Gwandu ya rera a 2018.

Kara karanta wannan

Ana fargabar masu kwacen waya sun kashe sojan Najeriya, tsohon sanata ya magantu

Wannan waka ta sa farin jinin Abba ya zarce cikin mabiya Kwankwasiyya, ta karkato da akalar ‘yan mata da matan aure a Kano.

5. Ko Gezau! Go gezau!!

A zaben 2023, wata waka da tayi tashe kuma ake ganin ta taimawa APC a Gombe ita ce ‘Ko Gezau’ wanda ‘Dan Musa Gombe ya rera.

Wannan waka ta ba magoya bayan Inuwa Yahaya kwarin gwiwa a lokacin da ya fuskanci barazana daga jam’iyyun PDP da NNPP.

Tarihin dangin Yar'adua a siyasa

Malam Musa Yar’adua shi ne Matawallen Katsina, ku na da labarin cewa ta zuri’arsa mai albarka an samu shugabanni da yawa a yau.

A gidansa aka samu Shehu Musa Yar’adua, Ummaru Musa Yar’adua da Abdulaziz Musa Yar’adua da kuma Murtala Shehu Musa Yar’adua.

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng