Ramadan: Gwamnan APC Ya Ware N2.8bn Domin Dafa Abincin Buda Baki, Ya Kafa Kwamiti

Ramadan: Gwamnan APC Ya Ware N2.8bn Domin Dafa Abincin Buda Baki, Ya Kafa Kwamiti

  • Gwamnan jihar Jigawa Umar Namadi ya bayyana kudurinsa na ciyar da talakawa da marasa galihu a jihar na tsawon kwanakin watan Ramadan
  • Gwamna Namadi ya amince da kashe Naira biliyan 2.8 domin gudanar da shirin buda bakin yayin da ya kafa cibiyoyin ciyar da abinci guda 609
  • Legit Hausa ta tattauna da Bamai Dabuwa, daga mazabar Kirikasamma da ke jihar Jigawa domin jin ra'ayinsa kan wannan shirin ciyarwa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Jihar Jigawa - Gwamnan jihar Jigawa Umar Namadi ya ware Naira biliyan 2.83 domin girka abincin buda baki na musamman a wannan wata na Ramadan.

Gwamnan ya ce ya kudiri aniyar shirya abincin buda bakin ne domin ciyar da talakawa da marasa galihu a jihar.

Kara karanta wannan

Halin kunci: Gwamnan APC zai rage farashin kayan abinci da 25% yayin da aka fara azumi

Gwamnatin Jigawa za ta ciyar da mutane a watan Ramadan.
Mutane 182,700 gwamnatin Jigawa za ta rika ciyarwa a Ramadan. Hoto: Umar Namadi
Asali: Twitter

Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa kwamishinan yada labarai na jihar jigawa, Sagir Musa ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Manufar wannan shirin ciyarwan Ramadan

Kwamishinan ya bayyana cewa an dauki matakin ne yayin zaman majalisar zartarwar jihar a ranar Laraba.

A cewarsa, shirin ciyarwar a lokacin azumi zai rage radadin da tashin farashin abinci ya haifar wa al'ummar jihar.

Musa ya ce an kafa cibiyoyin ciyar da abinci guda 609, inda za a mayar da hankali wajen samar da abinci kala uku ga talakawa da marasa galihu 182,700 a kullum.

Ramadan: Mutane miliyan 3.8 za su amfana

Daily Post ta ruwaito kwamishinan na cewa za a samar da cibiyoyin ciyar da abinci na musamman a dukkanin manyan makarantun jihar 10.

Ya kuma bayyana cewa za a aiwatar da shirin ciyarwar ne na tsawon makwanni uku inda ake fatan mutane miliyan 3.8 ne za su ci gajiyar shirina

Kara karanta wannan

Cushe a kasafin 2024: PDP ta bukaci Akpabio ya yi murabus, an samu karin bayani

Majalisar zartarwar jihar Jigawa ta kuma ware Naira biliyan 1.125 domin siyan karin shinkafa da taliya da za a ajiye na 'ko ta kwana' domin samar da isasshen abinci a fadin jihar.

An kafa cibiyoyi 2 a kowace gunduma

Tun da fari, Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa gwamnatin Jigawa ta ce za ta ciyar da mutane 171,900 a kullum a cikin watan Ramadan.

Gwamna Umar Namadi, ya bayyana haka a wajen bikin raba kayan tallafi ga mazauna garin Dutse da ke jihar Jigawa.

Ya ce gwamnati ta samar da cibiyoyi biyu a kowace gundumar zabe domin gudanar da shirin, inda ya ce kowace cibiya ana sa ran za ta ciyar da akalla mutane 300 a kullum.

Abun da 'yan Jigawa ke cewa

Bamai Dabuwa, daga mazabar Kirikasamma da ke jihar Jigawa ya ce wannan shirin ciyarwa zai zama hanyar samun abinci ga talaka da almajirai a jihar.

Kara karanta wannan

Ramadan 1445: Gwamnatin Jigawa ta dauki matakin saukakawa ma’aikata da azumi

A cewarsa, mutane na cikin wani mawuyacin hali na rashin kudi da abinci, yayin da a hannu daya kayan abinci suka yi tsada a kasuwa.

"Wannan abu ne mai kyau, musamman idan ka lura da cewa mutane suna cikin mawuyacin hali, ciyar da su a wannan matan ba karamin taimaka wa zai yi ba.
"Akwai almajirai da marasa galihu, kuma na ji an ce za zabi masallatai biyu a kowacce maza ba don raba wa mutane 600 abinci, gaskiya an taimaka sosai."

Duk da cewa har yanzu ba a kai ga fara rabon abincin ba, a cewar Dabuwa, gwamnatin Jigawa ta yi abun da ya dace na taimakawa talaka a irin wannan lokaci.

Jigawa: An rage lokutan zuwa aiki

A wani labarin, Legit Hausa ta ruwaito cewa gwamnan jihar Jigawa, Umar Namadi, ya rage lokutan da ma'aikatan jihar za su rinka zuwa aiki da tashi a wannan wata na Ramadan.

Gwamnan ya yi nuni da cewa rage lokutan zuwa aikin zai ba ma'aikata damar gudanar da ibadar azumi cikin kwanciyar hankali.

Asali: Legit.ng

Online view pixel