Yobe: Mayakan Boko Haram Sun Kai Hari a Cibiyar Tattara Sakamakon Zabe, Sun Kashe Mutum 2

Yobe: Mayakan Boko Haram Sun Kai Hari a Cibiyar Tattara Sakamakon Zabe, Sun Kashe Mutum 2

  • Rahotanni a safiyar Lahadi na nuni da cewa Boko Haram ta kai farmaki wata cibiyar tattara sakamakon zabe da ke jihar Yobe
  • A yayin harin, an ruwaito cewa sun kashe mutane biyu nan take, daga bisani kuma jami'an tsaro sauka fatattake su
  • Hukumar zabe ta kasa (INEC) na tsaka da tattarawa tare da sanar da sakamakon zaben cike gurbin majalisar Yobe ta Gabas aka kai harin

Sani Hamza, kwararren edita ne a fanni n nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Yobe - Mayakan Boko Haram sun kashe mutum biyu a a wata cibiyar tattara sakamakon zabe da ke Kuareta, kilo mita 20 nesa da garin Damaturu.

Gwamnatin jihar Yobe ta tabbatar da kai wannan farmaki a garin da ke kan hanyar Damaturu zuwa Maiduguri, kamar yadda shafin talabijin na AIT ya ruwaito.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Katsina ta dauki gagarumin mataki bayan 'yan bindiga sun kwashe 'yan kai amarya 60

Boko Haram ta kashe mutum biyu a Yobe
Ana tsaka da tattara sakamakon zabe a Yobe, Boko Haram ta kai farmaki an kashe mutum biyu.
Asali: Getty Images

A cewa hadimin gwamnan jihar kan tsaro, Manjo Janar Dahiru Abdulsalam (mai ritaya), Boko Haram ta kai harin ne a safiyar ranar Lahadi, 4 ga watan Fabrairu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An ruwaito cewa hukumar INEC na tsaka da tattarawa tare da sanar da sakamakon zaben cike gurbi na mazabar Yobe ta Gabas a majalisar dattijai lokacin da aka kai harin.

Sai dai Manjo Janar Abdulsalam ya bayyana cewa jami'an tsaro sun kai daukin gaggawa a cibiyar, inda suka fatattaki mayakan.

Gwamna Buni ya gamsu da zaben cike gurbi a jihar

Tun da fari, TV360 Nigeria ta ruwaito cewa gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya bayyana gamsuwarsa kan yadda aka gudanar da zaben cike gurbi a mazabar Yobe ta Gabas a ranar Asabar.

Buni wanda ya kada kuri’a a rumfar zabe ta Bulturi-Yerimari da ke Buni-Gari a karamar hukumar Gujba, ya ce ya yi farin ciki da fitowar masu kada kuri’a.

Kara karanta wannan

Murna ta koma ciki bayan kotu da datse dan PDP shiga takarar Sanata saura kwanaki 2 zabe

Gwamnan ya kuma ce yankin da a da aka dai-daita su a halin yanzu suna zaune cikin zaman lafiya, kuma suna gudanar da harkokin yau da kullum yadda ya kamata.

Sojoji sun kama shugaban matasa a Ebonyi

A wani labarin kuma, sojoji sun kama wani shugaban matasa a karamar hukumar Afikpo da ke jihar Ebonyi a daren ranar da za a gudanar dazaben cike gurbi a jihar.

Jam'iyyar AFGA ta yi ikirarin cewa ana amfani da sojoji waje cin zarafin mutane a yayin gudanar da zaben a jihar.

Asali: Legit.ng

Online view pixel