Majalisar Jihar PDP Ta Bukaci Cafke Shugaban Fulani Kan Wasu Dalilai 2, Ta Bayyana Zarge-zargen

Majalisar Jihar PDP Ta Bukaci Cafke Shugaban Fulani Kan Wasu Dalilai 2, Ta Bayyana Zarge-zargen

  • Serikin Fulanin yankin Iwajowa a jihar Oyo ya shiga matsala bayan Majalisar jihar ta nemi a kamo shi
  • Ana zargin Seriki Chumo da hannu a kisan wani manomi da kuma jami'in tsaron Amotekun da ke jihar a watan Oktobar 2023
  • Har ila yau, ana zargin Seriki da kasuwancin siyar da bindigu a yankin wanda hakan ya kara saka shakku a zukatan mutanen yankin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Oyo - Majalisar jihar Oyo ta bukaci cafke shugaban Fulani kan zargin kisan manomi da jami'in tsaro.

Majalisar ta tura sakon ne ga kwamishinan 'yan sanda a jihar da ya kama Seriki Chumo na karamar hukumar Iwajowa a jihar.

Kara karanta wannan

Yadda ficewar Nijar, Mali da Burkina Faso daga ECOWAS zai kawo matsaloli a Afrika

Za a kama shugaban Fulani kan kisan kai da hadin baki
Za a Seriki Chumo da ke shugabantar Fulani. Hoto: Seyi Makinde.
Asali: Facebook

Mene ake zargin shugaban Fulani a Oyo?

Ana zargin Chumo da hadin baki wurin kisan manomi da jami'in tsaron Amotekun a rikicin da aka yi a Iwere-Ile a watan Oktoban 2023.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamitin Majalisar kan harkokin tsaro ya fitar yayin zaman Majalisar.

Rahoton ya ce kama Seriki Chumo ya zama dole bayan samun wasu makamai a gidansa, kamar yadda The Nation ta tattaro.

Kudirin cafke shugaban Fulani ya isa Majalisa

Har ila yau, ana zargin Seriki da kasuwancin siyar da bindigu a yankin wanda hakan ya kara saka shakku a zukatan mutanen yankin.

Mamban Majalisar da ke wakiltar mazabar Iwojowa, Hon. Ogunsola Anthony shi ya gabatar da kudirin a matsayin matsala da ke da muhimmanci wanda ya kamata a bai wa kulawa, cewar Independent Newspaper.

Kara karanta wannan

Kamar Kano, Gwamnatin Kebbi ta fara yi wa zawarawa auren gata

Wannan na zuwa ne yayin da yankin Kudu maso Yammacin Najeriya ke fama da hare-haren 'yan bindiga a 'yan kwanakin nan da muke ciki.

'Yan bindiga sun hallaka sarakuna 2

Kun ji cewa wasu mahara sun hallaka manyan sarakunan gargajiya guda biyu a jihar Ekiti.

Lamarin ya faru ne a ranar Litinin 29 g watan Janairu yayin da suke dawowa daga wata ganawar tsaro a wani yankin.

Maharan sun farmaki sarakunan ne su uku yayin da daya daga cikinsu ya tsira da kyar inda suka hallaka sauran guda biyun.

Asali: Legit.ng

Online view pixel