Babban Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Damana Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

Babban Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Damana Ya Riga Mu Gidan Gaskiya

  • Allah ya karbi rayuwar Sheikh Usman Abubakar Damana a yau Laraba 3 ga watan Janairu a jihar Kebbi
  • Damana kafin rasuwarshi, shi ne babban limamin masallacin Juma'an Geese Phase 1 da ke birnin Kebbi
  • Za a gabatar da sallar jana'izarshi a masallacin Juma'an Geese Phase 1 da ke birnin Kebbi da misalin karfe biyu na rana

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kebbi - Da safiyar yau Laraba ce aka samu labarin rasuwar babban malamin addinin Musulunci a jihar Kebbi.

Marigayi Sheikh Usman Abubakar Damana ya rasu a yau Laraba 3 ga watan Janairu a birnin Kebbi, cewar Dokin Karfe TV.

Allah ya karbi rayuwar babban malamin addinin Musulunci a Kebbi
Babban Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Damana Ya Rasu. Hoto: Sheikh Usman Abubakar Damana.
Asali: Facebook

Waye ne Sheikh Usman Damana a Kebbi?

Kara karanta wannan

Miyagu sun harbe babban limamin Masallacin Jumu'a da ɗan acaɓa a Filato

Kafin rasuwarshi, shi ne babban limamin masallacin Juma'an Geese Phase 1 da ke birnin Kebbi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Har ila yau, shi ne mataimaki na biyu a kungiyar Izala a jihar Kebbi baki daya, cewar JIBWIS Gombe.

Za a gabatar da sallar jana'izarshi a masallacin Juma'an Geese Phase 1 da ke birnin Kebbi da misalin karfe biyu na rana.

Mutuwar malamin ta daga hankulan mutane ganin irin gudunmawar da ya bai wa addinin Musulunci a harkar karatuttukansa

Mutuwar Sheikh Giro ta girgiza al'ummar Musulmai

Wata majiya ta tabbatar da cewa a jiya ma sai da malamin ya gudanar da karatu da ya saba yi tsakanin mangariba da isha.

Har ila yau, Allah ya karbi rayuwar babban malamin addinin Musulunci a jihar Kebbi, Sheikh Abubakar Giro Argungu.

Giro ya rasu ne a watan Satumba bayan fama da jinya na tsawon lokaci a birnin Kebbi da ke jihar.

Kara karanta wannan

Bayan shafe shekaru 7 a kulle, an sake bude masallacin Juma'a da gwamnan PDP ya shiga lamarin

Mutuwar malamin ta girgiza al'ummar Musulmai a kasar baki daya ganin irin gudunmawar da ya bayar a ci gaban Musulunci.

Babban limami ya rasu a Gombe

A wani labarin, Babban limamin masallacin Juma'a a Unguwar Abuja da ke birnin Gombe ya riga mu gidan gaskiya.

Marigayin Sheikh Imam Sa'idu Abubakar ya rasu a birnin Gombe bayan dama da jinya.

Gwamna Inuwa Yahaya ya nuna alhininsa kan wannan babban rashi inda ya tura sakon jaje ga iyalan mamacin.

Asali: Legit.ng

Online view pixel