“Ba Ma Fada”: Kawaye Biyu Da Ke Soyayya Da Saurayi Daya Sun Yada Bidiyonsu a Gado
- Jama'a sun yi cece-kuce kan bidiyon wani mutum da ke soyayya da wasu kawaye biyu
- An gano su uku kwance suna sharholiya a bidiyo, lamarin da ya ja mutane suka yi masu caaa a kai
- Wasu mutane na tunanin yan matan na tare da mutumin ne saboda kudinsa, yayin da wasu suka yi martani kan yanayin jikinsu
Yan Najeriya sun yi martani a kan wani bidiyo da ke nuna wani mutum da ke soyayya da kawaye biyu a lokaci guda.
Wani shafin Instagram, @naijaeverything, ya yada bidiyon a dandalin soshiyal midiya, inda ya kara da cewar yan matan ba sa fada da junansu.
![Wasu kawaye biyu na soyayya da saurayi daya Wasu kawaye biyu na soyayya da saurayi daya](https://cdn.legit.ng/images/1120/98ea64604098a0d1.jpeg?v=1)
Asali: Instagram
Shafin ya kara da cewar yan matan sun nuna cewa yana da kyau ka so wa dan uwanka abun da kake so wa kanka.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/1e986c83e72dd36c.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
“Ba Ki Da Hankali Ne?” Wani Mutum Ya Kurma Ihu Bayan Ya Kama Mai Aiki Tana Wanke Masa Kayan Wuta Da Sabulu
"Ah ah!! kawaye 2 suna da saurayi daya kuma ba sa fada. Yau na tabbatar da cewa ka so wa dan uwanka abun da kake so wa kanka," @naijaeverything ya rubuta.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A cikin bidiyon, yan matan biyu sun sumbaci labban mutumin yayin da suke sharholiya a kan gadon.
Kalli bidiyon a kasa:
Jama'a sun yi martani
moni.solab ta ce:
"Idan dai har gayen ya siya masu gashin kanti su dukka biyun...ba za a samu sabani ba."
elenna__.sz ta ce:
"Yana da kyau ka so wa dan uwanka abun da kake so wa kanka amma akwai zaman lafiya a cikin samun na kanka."
olasumbo_goldinteriors ta ce:
"Wasu da suka fito gidan kishiyoyi za su dunga zaginsu."
ke___lv1 ta ce:
"Ya Allah gani nan kuma ina sake gode maka da baka bari wani dan uwana ya kunyatani ba a soshiyal midiya. Ina kaunarka Yesu."
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/39278057c3b6b15f.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Bidiyon Yan Mata Fiye Da 10 a Kan Babura Ya Girgiza Intanet, Sun Jeru Sanye Da Anko
wizdomgrams ya ce:
"Ku rabu da shi....da zaran kudi ya kare, idonsa zai bude."
Dan Najeriya zai auri mata biyu a rana daya
A wani labarin, mun ji cewa wani matashi dan Najeriya Mai suna Prince Okebulu Ndukwo Nkobi, zai yin wuff da tsala-tsalan yan mata biyu a rana daya.
Za a daura auren ne a jihar Abia cikin watan Nuwamba mai kamawa, a harabar gidan iyalin Nkobi da ke garin Abariba a jihar Anambra.
Asali: Legit.ng