“Aikin Mijinta Ne”: Hotunan Yadda Ayarin Motocin Matar Gwamnan Bauchi Suka Makale a Tabo

“Aikin Mijinta Ne”: Hotunan Yadda Ayarin Motocin Matar Gwamnan Bauchi Suka Makale a Tabo

  • Matar gwamnan jihar Bauchi, Hajiya Aisha Bala Muhammad, ta haddasa cece-kuce a soshiyal midiya kan wani mummunan al'amari da ya faru kwanan nan
  • Hotunan ayarin motocinta da suka makale a ambaliyar ruwa a hanyarta ta zuwa kaddamar da wani cibiyar lafiya a jihar sun yadu
  • Yayin da wasu suka alakanta halin da ta shiga da mugun shugabancin mijinta a jihar, wasu sun roki Allah ya shiga lamarin siyasar Najeriya

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Jihar Bauchi - Ayarin motocin matar gwamnan jihar Bauchi, Hajiya Aisha Bala Muhammad, sun makale a cikin ambaliyar ruwa a hanyarsu ta zuwa tafiya.

Ayarin motocin matar gwamnan Bauchi sun makale a tabo
“Aikin Mijinta Ne”: Hotunan Yadda Ayarin Motocin Matar Gwamnan Bauchi Suka Makale a Tabo Hoto: @dipoaina1
Asali: Twitter

Wani mai amfani da manhajar X Ainà Dipo @dipoaina1 ya tabbatar da lamarin a wata wallafa da ya yi a shafinsa tare da hotunan.

A cikin rubutun nasa wanda Legit.ng ta gano, ya alakanta halin da matar gwamnan Bauchin ta shiga da irin abun da ya faru da Gwamna Godwin Obaseki na jihar Edo.

Kara karanta wannan

Zan taimake ku: Tinubu ya mika sakon jajantawa da karfafa gwiwa ga sarkin Moroko

A jawabin nasa, ya bayyana cewa "wannan zai fada maku abubuwa da dama cewa jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) da abun da take wakilta."

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

"Allah ya kawo sauki," inji Dipo.

Yan Najeriya sun yi martani yayin da ayarin motocin matar gwamnan jihar Bauchi suka makale a tabo

Legit.ng ta tattaro wasu daga cikin ra'ayoyin jama'a game da lamarin bayan an wallafa shi a manhajar X wacce aka fi sani da Twitter a baya.

@Sunigab ya rubuta:

"Aikin mijinta ne. Kada ta yi mamaki."

@esin_kings32147 ya rubuta:

"Matar gwamnan jihar Bauchi, Hajiya Aisha Bala Muhammad a hanyarta ta zuwa Jamdan don kaddamar da wani cibiyar lafiya.

"Abun bakin ciki."

@munir__ell ya ce:

"Abun takaici idan babu hanya mai kyau da za a kai kayan asibiti da magunguna da kuma hanyar da garuruwan makwabta za su dunga zuwa cibiyar wannan wani abun kunya ne."

Kara karanta wannan

Da Ɗumi-Ɗumi: Hatsarin Jirgin Ya Laƙume Rayukan Mutane Sama da 10 a Jihar Arewa

Mata 340 ne suka lakadawa mazajensu duka a jihar Lagas

A wani labari na daban, mun ji cewa gwamnatin jihar Lagas ta ce akwai karin rahotanni 340 na mata masu lakadawa mazajensu mugun duka a cikin shekara daya da ta gabata, Satumban 2022 da Yulin 2023.

Titilola Vivour-Adeniyi, shugabar hukumar yaki da cin zarafin mutane ta jihar Lagas, ce ta bayyana haka, jaridar PM News ta rahoto.

Asali: Legit.ng

Online view pixel