Tsohon Shugaban Kasa Ya Fadi Babban Abin da Yake Sa Jami'ai Tafka Sata a Gwamnati

Tsohon Shugaban Kasa Ya Fadi Babban Abin da Yake Sa Jami'ai Tafka Sata a Gwamnati

  • Babu abin da ke jawo wadanda ke aikin gwamnati suyi sata irin tsoron halin da za su shiga bayan ritaya
  • Dr. Goodluck Jonathan yana ganin a dalilin wannan, ma’aikata suke saba doka domin su tanadi dukiya
  • Jonathan ya soki yadda dokokin Gwamnati suka haramtawa ma’aikatan gwamnatin yin kasuwanci

Abuja – A makon nan Goodluck Jonathan yace tsoron abin da zai faru da rayuwarsu bayan sun yi ritaya, shi yake jawo ma’aikatan gwamnati suyi sata.

Vanguard tace Dr. Goodluck Jonathan ya yi wannan jawabi ne da yake bayani a wajen kaddamar da wani littafi da Obioma Onwuzurumba ya rubuta.

Onwuzurumba wanda ya yi aiki a matsayin Fasto a fadar shugaban kasa ya rubuta littafi wanda aka kaddamar a ranar da ya cika shekaru 73 a Duniya.

An kira tsohon shugaban kasar ya gabatar da jawabi na musamman a ranar, a nan ne ya tattauna a kan rashin gaskiyar da ma’aikatan gwamnati suke yi.

Kara karanta wannan

A Karshe ‘Dan Takaran APC, Tinubu Ya Yi wa Duniya Bayanin Yadda Ya Mallaki Dukiyarsa

Ya makoma za ta kare?

"Daga cikin manyan matsalolin da muke da su a Najeriya, kuma watakila yake jawo ake rashin gaskiya sosai shi ne rashin sanin yadda gobe za ta kasance.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Saboda haka sai mutane su ce tun da yanzu ina aiki, bari in taimaki kai na ta muguwar hanya."

- Dr. Goodluck Jonathan

Tsohon Shugaban Kasa
Dr. Goodluck Jonathan a taron ECOWAS Hoto: @GEJonathan
Asali: Twitter

Jonathan ya yabawa Obioma Onwuzurumba

Tribune tace Dr. Jonathan ya ji dadin ganin yadda Onwuzurumba da mai dakinsa suka kafa cibiyar da za ta rika kula da tsofaffin mutanen cikin al’umma.

A jawabinsa, tsohon shugaban na Najeriya ya kuma koka a kan yadda dokar kasa take hana ma’aikatan gwamnati yin kasuwanci a lokacin da suke aiki.

"Baya ga haramta masu yin kasuwanci, idan ma’aikatan sun yi ritaya, ba a kula da su sosai.

Kara karanta wannan

Dole Ta Yi Masa? Ango Ya Yi Jugum Yana Kallon Amaryarsa Yayin da Take Girgijewa Ita Kadai A Bidiyo

Babu wani tsarin kula da walwalar al’umma. Musamman idan ka duba mutanen da ke aikin tsaro, misali a yau na saurari wata hira a gidan rediyo.
Kuma dokokinmu ba su barin ma’aikatan gwamnati su kafa kamfani, illa noma. An hana ka kasuwanci da ka na aiki, ka gama aiki, ba a kula da kai."

- Dr. Goodluck Jonathan

Rahoton yace Farfesa Jerry Gana ya yi jawabi a wajen taron, shi ma ya koka da cewa yanzu mutanen da ake da su masu gaskiya da mutuncin sun yi karanci.

Sanata Anyim Pius Anyim, Ama Pepple da Fastoci irinsu Henry Ndukuba da Archbishop Peter Akinola sun zo wajen bikin kaddamar da wannan littafi.

Ina da kudi, ba zan musanya arziki na ba - Tinubu

A jiya ne aka samu labari cewa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya amsa zargin da ake yi masa na samun dukiya ta hanyar yin sata da kuma taba baitul-malin Legas.

Kara karanta wannan

Abubuwan da Atiku, Obi, Kwankwaso Suka Fada a Taron 'Yan Takaran 2023

‘Dan takarar na APC yace babu hujjar da ke nuna ya ci kudin gwamnati, yace a sanadiyyar hannun jari da gado ya zama Attajiri har ‘yan adawa suke hassada.

Asali: Legit.ng

Online view pixel