NIN: Yadda Kujerar Minista Ta Jawowa Isa Ali Pantami Barazanar Kisa a Najeriya
- Isa Ali Ibrahim Pantami ya shigo da tsarin yin rajistar NIN a wayoyin salula domin a inganta tsaro
- Wannan mataki da Ministan sadarwa da tattalin arzikin zamanin kasar ya dauka, ya zo da irin farashinsa
- Wasu sun fito suna barazana ga rayuwar Isa Ibrahim Pantami saboda yace dole ayi wa layin SIM rajista
Abuja - Ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani, Isa Ali Ibrahim Pantami yayi bayanin kalubalen da ya fuskanta saboda ya kawo tsarin NIN.
A ranar Juma’a 16 ga watan Satumba 2022, Daily Trust ta rahoto Isa Ali Ibrahim Pantami yana cewa ya fuskanci barazanar kisa a kujerar Minista.
Pantami yace yunkurin yi wa kowane layin waya rajista da lambar NIN ta jawo masa wannan barazana.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/8f56463e802921a7.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Peter Obi Ya Yi Magana Da CNN, Ya Bayyana Tanadin Da Ya Yi Wa Arewacin Najeriya Idan Ya Zama Shugaban Kasa
Ministan ya bayyana haka ne a wajen wani taro na musamman da hukumar NIMC mai tattara bayanan ‘yan kasa ta shirya a birnin tarayya Abuja.
Barazana har a rediyo
A cewar Dr. Isa Pantami, ta kai an fito baro-baro a gidan rediyo ana yi masa barazana, ba don komai ba sai saboda ya shigo da tsarin yin rajistar NIN.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Kamar yadda Ministan ya fada, wannan baranza bai sa ya janye yunkurinsa ba domin ya san babu mai iko da rayuwar ‘Dan Adam sai Ubangiji.
![Isa Ali Ibrahim Pantami Isa Ali Ibrahim Pantami](https://cdn.legit.ng/images/1120/21fe9f3e276cdc74.jpeg?v=1)
Asali: Twitter
Jawabin Minista a taron NIMC
“Za mu cin ma nasara a bangaren tattalin arzikin zamani ne a lokacin da muka yi kokari wajen ganin mutane sun shiga cikin kundin bayanan kasa.
A lokacin da muka fara aikin nan, mutane da-dama sun juya mani baya. An yi wa rayuwata barazana a gidan rediyon BBC saboda shigo da tsarin.
Na tsaya tsayin-daka domin nayi imani babu wanda ke da iko da rayuwata sai Allah madaukaki.
Kokarin da NIMC take yi a yau
Jaridar Leadership tace shugaban NIMC, Injiniya Aliyu Aziz ya gabatar da jawabi a wajen taron, ya yi bayanin yadda suke kokarin wayar da kan jama’a.
Aliyu Aziz yake cewa suna hada-kai da sarakunan gargajiya da masarautu domin mutane su san muhimmancin yin rajista katin NIN na ‘yan Najeriya.
Barazanar Boko Haram
A shekarun baya, an ji labarin yadda shugaban Boko Haram, Abubakar Shekau ya yi barazanar kashe Ministan sadarwa, Isa Ali Pantami da Bulama Bukarti.
Shekau ya bayyana haka ne a cikin wani sabon bidiyo daya fitar mai tsawon mintuna 15, ya caccaki Sheikh Isa Ali Pantami saboda tsarin da ya kawo.
Asali: Legit.ng