Dantata: Jerin Mutanen da Suka Mutu a Wasu Kasashe aka Birne Su a Madina

Dantata: Jerin Mutanen da Suka Mutu a Wasu Kasashe aka Birne Su a Madina

  • Birne Aminu Alhassan Dantata a kasa mai tsarki ya sanya mutane waiwaye ga tarihi domin duba mutanen da aka kai su Madina bayan rasuwarsu a wata kasa
  • An birne fitaccen attajirin Najeriya, Alhaji Aminu Dantata a makabartar Baƙi'a da ke Madina bayan rasuwarsa a Hadaddiyar Daular Larabawa
  • Tsohon shugaban Tunisiya, Ben Ali, da kuma Muhammad al-Badr daga Yemen, su ma an birne su a ƙasa mai tsarki ta Madina bayan rasuwarsu

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja - Madina, ƙasa mai tsarki ga Musulmai, tana da tarin tarihi da ɗaukaka saboda kasancewar birnin da Manzon Allah (SAW) ya rayu kuma aka birne shi.

A dalilin haka, wasu fitattun mutane daga kasashen duniya suna buƙatar a birne su a can bayan mutuwarsu, musamman waɗanda suka sadaukar da rayuwarsu wajen hidimar addini da jama'a.

Aminu Dantata da Muhammad Al-Badar da aka birne a Madina
Aminu Dantata da Muhammad Al-Badar da aka birne a Madina. Hoto: Mohammed Hassan|Getty Images
Asali: Facebook

A wannan rahoton, mun kawo muku jerin mutanen da suka mutu a ƙasashen ƙetare amma aka ɗauki gawarsu zuwa Madina don a birne su.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

1. Dantata ya cika burin birne shi a Madina

Aminu Dantata, fitaccen ɗan kasuwa kuma ɗan ƙasa mai kima daga Najeriya, ya rasu a ranar Asabar a birnin Abu Dhabi na UAE yana da shekaru 94.

Bayan samun amincewar gwamnatin Saudiyya, an ɗauko gawarsa zuwa Madina inda aka yi masa salla a masallacin Annabi kafin a birne shi a maƙabartar Baƙi’a.

BBC ta wallafa cewa Alhaji Dantata ya bar mata uku, 'ya'ya 21 da jikoki 121 kuma jigo ne a harkokin kasuwanci da jin kai.

Marigayi Aminu Alhassan Dantata kafin rasuwar shi
Marigayi Aminu Alhassan Dantata kafin rasuwar shi. Hoto: Mohammed Hassan
Asali: Twitter

A shekarar da ta gabata, Aminu Dantata ya ba da Naira biliyan 1.5 ga wadanda ambaliya ta shafa a jihar Borno.

2. An birne Al-Badr na Yemen a Madina

Wani shugaba daga Yemen, Muhammad al-Badr ya samu darajar birne shi a Madina bayan rasuwarsa a London a shekarar 1996 kamar yadda rahoton Asharq ya tabbatar.

Al-Badr, wanda aka haifa a Hajjah, Yemen a shekarar 1929, ya shahara da kishin addini da kuma karatun ilimin addini.

Ko da yake mulkinsa bai wuce mako guda ba a shekarar 1962 kafin ya fuskanci juyin mulki, an girmama shi har zuwa mutuwarsa.

Jaridar Indepedent ta wallafa cewa Al-Badr ya bar 'ya'ya maza biyu, mata biyu a lokacin da ya rasu a ranar 6 ga Agustan 1996 a London.

Muhammad Al-Badr a shekarar 1957
Muhammad Al-Badr a shekarar 1957. Hoto: Getty Images
Asali: Getty Images

3. An birne Ben Ali na Tunisiya a Madina

Tsohon shugaban Tunisiya da ya mulki ƙasar daga 1987 zuwa 2011, Zine El Abidine Ben Ali ya rasu a Saudiyya bayan ya gudu daga kasarsa sakamakon bore da rikice-rikicen da suka faru.

France 24 ta ce Ben Ali ya rasu ne a Saudiyya ba a wata kasa ba, amma an dauko gawarsa daga Jiddah zuwa makabartar Baƙi’a a Madina, kusa da masallacin Annabi Muhammadu (SAW).

Mutuwar wani matashi mai sayar da kaya a shekarar 2010 a Sidi Bouzid ya tayar da bore wanda ya kai ga Ben Ali gudu zuwa Saudiyya, inda ya yi zaman gudun hijira har ya rasu.

Tsohon shugaban Tunisiya, Zine El Abidine Ben Ali
Tsohon shugaban Tunisiya, Zine El Abidine Ben Ali. Hoto: Getty Images
Asali: Getty Images

Hukuncin kai gawa zuwa Madina a Musulunci

A wani rahoton, kun ji cewa wani malamin addinin Musulunci a Najeriya, Sheikh Aliyu Muhammad Sani ya yi bayani kan hukuncin kai gawa zuwa kasa mai tsarki.

A jawabin da ya yi, malamin ya ce babu laifi a Musulunci a kai gawa zuwa kasa mai tsarki kamar Madina ko Makka.

Sheikh Aliyu ya kara da cewa malamai sun tabbatar da hakan musamman lura da Annabi Musa (AS) ya nemi a kai gawarsa Kudus domin masa jana'iza.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng