Latest
Mutane sun wayi gari cikin mawuyacin hali na ƙarancin man fetur a jihar Kaduna wanda ya sa ƴan bunburutu suka buɗe sabuwar kasuwa da farashi mai tsada.
Daga cikin masu neman takarar kujerar gwamnan jihar Ondo karkashin PDP, tsohon mataimakin gwamnan jihar, Agboola Ajayi ya lashe tikitin takarar jam'iyyar.
MTN, Glo, Airtel da 9 Mobile sun koka kan yadda kudin da suke caja a yanzu ba ya isa su gudanar da ayyukansu. Kamfanonin na duba yiwuwar kara kudin kira, data da SMS
Wasu 'yan bindiga sun kai farmaki fadar Sarkin Zurmi a jihar Zamfara inda suka hallaka mutane uku yayin da suka lalata karfunan sabis a yankin yayin farmakin.
A yayin da take shirin gudanar da zaben kananan hukumomi, gwamnatin jihar Yobe karkashin Gwamna Mai Mala Buni ta rusa shugabannin riko 17 da kansilolinsu.
An shiga wani irin yanayi bayan rasuwar tsohon sanata a jihar Enugu, Ayogu Eze wanda ya wakilci Enugu ta Arewa a Majalisar Dattawa daga shekarar 2007 zuwa 2015.
Wasu jiga-jigan jam'iyyar All Progressives Congress (APC) a shiyyar Arewa ta Tsakiya, sun bukaci Abdullahi Umar Ganduje ya yi murabus daga shugabancin jam'iyyar.
Babbar Kotun Tarayya ta yi fatali da korafin da aka shigar kan Ministar Al'adu, Hannatu Musawa game da rashin kammala bautar ƙasa yayin da aka naɗa ta mukami.
A yayin da gwamnatin Abba Yusuf ke karin haske kan kokarin da take yi na magance karancin ruwa a Kano, ta ce tana kashe akalla N1.2bn duk wata domin samar da ruwa.
Masu zafi
Samu kari