Bayan Dogon Jira, An Sanya Ranar Fara Haska Fim din 'Gidan Badamasi' Zango na 6

Bayan Dogon Jira, An Sanya Ranar Fara Haska Fim din 'Gidan Badamasi' Zango na 6

  • Kamfanin Dorayi Films ya sanar da dawowar shirin Gidan Badamasi zango na shida bayan gama zango na biyar a karshen 2022
  • Masu kallon wannan shirin sun kasance cikin tsumayin ganin zango na shida tun a 2023, amma ba su dace ba sai a shekarar nan
  • Falalu Dorayi ya bayyana cewa zango na shida zai kawo sababbin salo na barkwanci, yayin da ya saki wasu jerin tallace-tallace

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kano - A Disambar 2022, kamfanin Dorayi Films ya sanar da fitar shirin Gidan Badamasi zango na biyar, kashi na 13, wanda ya zama kashin karshe a zangon.

Tun da shekarar 2023 ta shiga, masu kallo ke ta tsumayin ganin zango na shida na shirin, amma babu labari har sai a watan Disambar 2024 da muke ciki.

Kara karanta wannan

An shiga tashin hankali a Kaduna yayin da wata mata ta kashe ƴarta da maganin ɓera

Falalu A Dorayi ya yi magana yayin da ake shirin dawo da shirin Gidan Badamasi.
Za a dawo haska shirin Gidan Badamasi zango na 6 daga 19 ga Disambar 2024. hoto: falalu_a_dorayi
Asali: Instagram

Gidan talabijin din Arewa24 ya yi sanarwa a shafinsa na Facebook, cewa zango na shida na shirin Gidan Badamasi zai dawo a tsakiyar Disamba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gidan Badamasi zango na 6 na nan tafe

A cewar sanarwar:

"Albishirin ku. Shirin Gidan Badamasi Zango na shida yana nan tafe a ranar 19 ga watan Disamba da misalin karfe 6:00 na yamma."

Sai dai kuma, gidan talabijin din ya nuna cewa shirin zai rika zuwa ne a kan manhajarsa ta Arewaondemand, ba tare da fadin ko za a rika haskawa a talabijin ba.

A mafi yawan lokuta, Arewa24 ba ta haska fina finan da take dorasu kacokan a kan manhajarta, misali shi ne shirin 'Wata Rana a Kano' na Abubakar Bashir Maishadda.

Kadan daga shirin Gidan Badamasi zango na 6

Mai shirya shirin Gidan Badamasi, Falau A. Dorayi ya wallafa wasu gajerun tallace tallace a shafinsa na Instagram da ta yi tsokaci kan shirin zango na shida.

Kara karanta wannan

'Yana da kwarin guiwa a 2027'; an fadi shirin da Tinubu ya yi game da zabe

A talla ta farko, an ga Tijjani Asase (Adamahama) da jaruma Hadiza Kabara (Hauwa) a cikin kayan gidan yarin, yayin da Falau ya wallafa cewa:

"Adahama da Hauwa an yi abin kunya, an tafi gidan yari."

A wata tallar kuma, an ga Yaya Dan Kwambo a cikin mota yana yiwa su Bazuka tsiya tare da barazanar daure su, yayin da Falalu ya yi bayani cewa:

"Wannan gudu ne tsakanin kare da zomo, wane ya saci kudi, wane na neman ya za ayi ya karbi kudinsa."

Jarumi kuma mai ba da umarni, Falalu A Dorayi ya nuni da cewa Gidan Badamasi zango na shida zai zo da abubuwan salo na barkwanci da ba a gani a baya ba.

Gidan Badamasi ya fito da jaruma Azeema

A wani labarin, mun ruwaito cewa jarumar Kannywood, Hauwa Ayawa ta sanar da cewa shirin Gidan Badamasi ne ya fito da tauraruwarta har ta yi haske.

Kara karanta wannan

Bayan an samu asarar rayuka, mazauna Kano sun shiga fargabar dawowar fadan daba

Hauwa da a yanzu aka fi sani da Azeema Gidan Badamasi ta taka rawar 'yar Alhaji Badamasi a shirin, kuma ta nuna kwarewa a matsayin da aka ba ta.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.