Jirgin Sama Dauke da Ma'aikatan Lafiya Ya Gamu da Hatsari Dukkan Mutanen ciki Sun Mutu

Jirgin Sama Dauke da Ma'aikatan Lafiya Ya Gamu da Hatsari Dukkan Mutanen ciki Sun Mutu

  • Mutane biyar, ciki har da matukin jirgi, likita, mataimakin ma’aikacin lafiya da ma’aikatan jinya biyu, sun mutu a hadarin
  • Jirgin BO-105 na Flying Doctor Service ya faɗi ne da yammacin Talata, kimanin kilomita 315 kudu maso gabashin birnin Miri
  • Hukumar binciken hadurran jiragen sama ta Malaysia za ta je wurin da hadarin ya faru domin gano musabbabin lamarin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Kasar Malaysia - Mutane biyar sun mutu bayan wani jirgin sama mai saukar ungulu ya faɗi a wani filin jirgi mai nisa a cikin jihar Sarawak, da ke arewa maso yammacin tsibirin Borneo a Malaysia.

Jami’an ƙasar sun tabbatar da cewa jirgin BO-105, wanda ke aiki da hukumar Flying Doctor Service, ya faɗi ne da yammacin Talata, 8 ga watan Satumban 2026.

Jirgin sama ya yi hatsari a Malaysia
Masu bincike a wurin wani hatsarin jirgin sama Hoto: @EVostox
Source: Twitter

Jirgin ya faɗi a yankin daji

Kara karanta wannan

Ana zargin Bello Turji da kai mummunan hari a Sokoto da aka sace mutane 40

Jami’an kula da bala’o’i sun ce hadarin ya faru ne kimanin kilomita 315 kudu maso gabashin birnin Miri, cewar rahoton tashar TRT Africa.

Galong Luang, shugaban hukumar kula da bala’o’i ta Miri, ya tabbatar da mutuwar dukkan mutanen da ke cikin jirgin.

“An tabbatar da cewa dukkan mutane biyar da ke cikin jirgin sun mutu, kamar yadda rahotannin Hukumar Kashe Gobara da Ceto da Ma’aikatar Lafiya suka tabbatar,” in ji Luang a cikin wata sanarwa.

Rahotannin kafafen yaɗa labarai na cikin gida sun bayyana cewa matukin jirgin, wani likita, mataimakin ma’aikacin lafiya da ma’aikatan jinya biyu na cikin mutanen da suka mutu.

An ga jirgin yana hayaƙi kafin ya faɗi

Wasu hotunan bidiyo da aka wallafa a kafafen sada zumunta sun nuna jirgin yana fitar da hayaƙi mai yawa jim kaɗan kafin ya faɗi. Sai dai har yanzu ba a bayyana musabbabin hadarin ba.

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Malaysia ta ce ƙungiyar da ke binciken hadurran jiragen sama za ta isa wurin da hadarin ya faru ranar Laraba, 9 ga watan Satumban 2026.

Kara karanta wannan

'Yan ta'adda sun bindige babban manajan banki a Najeriya har ya mutu

Ana sa ran binciken zai taimaka wajen gano abin da ya haddasa faɗuwar jirgin da kuma ko akwai wasu abubuwan da suka taimaka wajen faruwar lamarin.

Aikin Flying Doctor Service

Hukumar Flying Doctor Service ta Malaysia na taimaka wa al’ummomin ’yan asalin ƙasar da ke zaune a yankunan dazuzzuka masu yawan gaske da kuma wuraren da ke da wahalar isa.

Waɗannan al’ummomi sun dogara sosai da sufurin jiragen sama saboda yanayin dazuzzuka da kuma wahalar hanyoyin ƙasa a cikin yankunan ƙasar.

Tawagogin ma’aikatan lafiya kan ƙunshi likita, mataimakin ma’aikacin lafiya, ma’aikatan jinya da sauran jami’an lafiya.

Suna tafiya da jirgin sama mai saukar ungulu ko ƙaramin jirgin sama zuwa ƙauyuka da gidajen gargajiya a tsarin ziyara da ake gudanarwa kowane wata ko bayan wata biyu.

Aikin na da muhimmiyar rawa wajen kai ayyukan kiwon lafiya ga al’ummomin da ke zaune a yankunan da ke da nisa da cibiyoyin kiwon lafiya na yau da kullum.

Jirgin sama ya yi hatsari a Malaysia
Wasu mutane a wurin da jirgin saman Malaysia ya kona bayan yin hatsari Hoto: Sawarak Edisi Khas
Source: Facebook

Jirgin sama ya yi hatsari a Amurka

A wani labarin kuma, kun ji cewa wani jirgin dakon kaya na Amazon Prime Air ya yi hatsari a filin jirgin Miami International Airport.

Akalla mutane biyar sun mutu yayin da wasu biyar suka samu raunuka bayan da jirgin kirar Boeing ya gamu da hatsari.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng