Iran Ta Amince da Mika Muhimmin Arzikinta domin Yarjejeniya da Amurka

Iran Ta Amince da Mika Muhimmin Arzikinta domin Yarjejeniya da Amurka

  • Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta amince za ta mika tarin sinadarin uranium da aka tace sosai a kasar
  • Majiyoyi sun bayyana cewa hakan na da nasaba da yarjejeniyar da aka ce shugaban Amurka Donald Trump ya sanar
  • Rahotanni suka ce jami’an Amurka biyu sun tabbatar Iran na da isasshen uranium da zai iya kera bama-baman nukiliya guda 11

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Tehran, Iran - Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta amince da wani shiri na musamman domin tabbatar da yarjejeniya da Amurka.

Iran ta amince ta mika tarin sinadarin uranium da aka tace sosai a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar da shugaban Amurka, Donald Trump.

Jaridar New York Times ta rawaito cewa jami’an Amurka biyu sun bayyana Iran ta yarda da wata sanarwa da za ta tabbatar da mika uranium ɗin.

Kara karanta wannan

'Dan siyasar da ke zaune a Amurka ya samu takarar Majalisar wakilai a ADC

Rahoton ya bayyana cewa adadin uranium ɗin da Iran ke da shi zai iya isa a ƙera bama-baman nukiliya guda 11 idan aka yi amfani da shi.

Batun yadda za a kawar da uranium ɗin, wanda Trump ya kira “ƙurar nukiliya,” ya kasance babban abin da ya hana cimma matsaya cikin tattaunawar.

Yayin da Iran ke neman a fayyace makomar tarin uranium ɗinta bayan cimma yarjejeniyar dakatar da yaƙi, jami’an Amurka sun yi barazanar sake kai hare-hare.

Rahoton ya ce jami’an Amurka sun gargadi Iran cewa za su ci gaba da kai hare-hare idan har ta ƙi amincewa da mika sinadarin uranium ɗin.

Karin bayani na tafe....

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.