Yan Bindiga Sun Yi Ta’asa, Sun Hallaka Ministan Tsaron Mali yayin Hari a Gidansa
- Ministan tsaron Mali, Janar Sadio Camara, ya mutu bayan hare-haren hadin gwiwa kan sansanonin soji a sassa daban-daban
- Maharan da suka hada da kungiyoyin da ke da alaka da al-Qaeda da kuma mayaƙan Tuareg sun kai harin kunar bakin wake a gidansa da ke Kati
- Ana kallon mutuwar Camara a matsayin babbar illa ga rundunar sojin Mali, yayin da hare-haren ke ci gaba a wurare da dama
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Bamako, Mali - Ministan tsaron Mali, Janar Sadio Camara, ya rasu sakamakon hare-haren hadin gwiwa da aka kai kan wuraren soji a sassa daban-daban na kasar.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne bayan yan bindiga sun kai hari a gidansa da ke garin Kati, wanda ke kusa da Bamako a ranar Asabar 25 ga watan Afrilun 2026.

Source: Getty Images
An bayyana cewa wasu kungiyoyi masu alaka da al-Qaeda tare da mayaƙan Tuareg ne suka kai harin, inda suka yi amfani da motar kunar bakin wake wajen kai farmakin, cewar Al Jazeera.
Kati na daga cikin wuraren da ake ganin suna da tsaro sosai a Mali, amma duk da haka maharan sun samu damar kai wannan hari mai girma.
Masana sun bayyana Camara a matsayin daya daga cikin manyan jiga-jigan gwamnatin mulkin soja, wanda aka kafa bayan juyin mulki da aka yi a shekarun 2020 da 2021.
Rahotanni sun ce mutuwarsa babbar illa ce ga rundunar sojin Mali, musamman a daidai lokacin da ake fama da hare-haren kungiyoyin masu dauke da makamai.
Har yanzu ana ci gaba da jin karar harbe-harbe da fashe-fashe a wasu yankuna kamar Kidal da Gao, alamar cewa rikicin bai lafa ba, kamar yadda Reuters ta ruwaito.
Masana tsaro sun yi gargadin cewa ana iya samun karin fada kan iko da muhimman wurare a cikin kwanaki masu zuwa.
An kuma bayyana cewa kungiyoyin da a baya suke yaki da juna sun hada kai domin kai hare-hare kan gwamnatin Mali.
Kungiyar Tarayyar Afirka da sauran kungiyoyin kasa da kasa sun yi Allah wadai da wadannan hare-hare, suna kira da a dauki matakan gaggawa don dawo da zaman lafiya.
Wani ɗan uwa, da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce ministan da aƙalla mutum uku daga cikin iyalansa sun mutu sakamakon bam ɗin mota da wata ƙungiya mai alaƙa da Al Qaeda ta dasa.
Karin bayani na tafe....
Asali: Legit.ng

