Magana Ta Kare, Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Shekarau Ya Fice daga Jam'iyyar PDP
- Malam Ibrahim Shekarau ya mika takardar ficewarsa daga PDP ga shugabannin jam'iyyar a mazabarsa da ke karamar hukumar Nassarawa a Kano
- Tsohon gwamnan ya ce ya yanke shawarar fita daga PDP ne bayan tattaunawa da neman shawarwari daga abokan siyasarsa na kwamitin shura
- Duk da bai bayyana jam'iyyar da zai koma ba a hukumance, amma bayanai sun nuna an kewaye gidansa da tambarin jam'iyyar APC mai mulki
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Kano, Nigeria - Tsohon gwamnan Jihar Kano, Ibrahim Shekarau, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP a hukumance.
Shekarau ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi, 19 ga Afrilu, 2026 a gidansa da ke Mundubawa Avenue a Kano, bayan kwanaki na tuntuba da shawarwari da ya yi da magoya bayansa, ciki har da kwamitin Shura.

Source: Facebook
Shekarau ya mika takardar ficewa daga PDP
The Nation ta ruwaito cewa cikin wasiƙar murabus ɗin da ya rubuta ranar 19 ga Afrilu, 2026 wadda ya aika wa shugaban PDP na unguwar Giginyu a ƙaramar hukumar Nassarawa, ya ce matakin ya fara aiki nan take.
“Ina fatan za ku karɓi wannan wasiƙa a matsayin sanarwar ficewata daga jam’iyyar PDP daga yau,” in ji shi.
An kuma aika kwafin wasiƙar ga shugaban PDP na jihar Kano da na ƙaramar hukumar Nassarawa, domin sanar da su a hukumance, kamar yadda Daily Trust ta rahoto.
Dalilin tsohon gwamnan na barin PDP a Kano
Shekarau ya ce ya ɗauki wannan mataki ne bayan tattaunawa mai zurfi da mabiyansa, domin ci gaba da harkokinsu na siyasa a wata jam’iyya daban.
Rahotanni sun nuna cewa an kawata gidansa da fastocin jam’iyyar APC, abin da ke nuni da cewa yana shirin komawa jam’iyya mai mulki.
Shekarau, wanda ya yi wa’adin mulki biyu a matsayin gwamnan Kano daga 2003 zuwa 2011, ana sa ran zai sanar da komawarsa APC a hukumance nan ba da jimawa ba.
Tsohon gwamnan na daga cikin waɗanda suka kafa tsohuwar jam’iyyar ANPP, wadda ya yi takara a ƙarƙashinta ya kuma zama gwamna.

Source: Facebook
Wace jam'iyya Shekarau zai koma?
A shekarar 2014 ne Shekarau ya koma PDP bayan haɗewar jam’iyyun adawa, wadanda suka haifar da kafa APC.
Yanzu dai alamu na nuna cewa yana dab da komawa jam’iyyar APC domin ci gaba da harkokinsa na siyasa, amma dai har yanzu babu wata sanarwa a hukumance kan hakan.
Yadda APC ta yi zawarcin Shekarau
A wani rahoton, kun ji cewa shugaban Jam’iyyar APC na Kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya kai ziyara gidan Malam Ibrahim Shekarau da ke cikin jihar Kano.
A wannan ziyara, Yilwatda ya jaddada muhimmancin hadin kai a tsakanin shugabannin siyasa na Arewa, inda ya bayyana yankin a matsayin cibiyar siyasar Najeriya tare da rokon Shekarau da ya dawo APC.
Da yake maida martani, Shekarau ya jinjina wa tawagar APC bisa kawo masa ziyara har gida, yana mai cewa nan da kwanaki biyu zai yanke makomarsa ta siyasa
Asali: Legit.ng

