Zambia: Tsohon Shugaban Ƙasa, Lungu Ya Riga Mu Gidan Gaskiya Yana da Shekaru 68

Zambia: Tsohon Shugaban Ƙasa, Lungu Ya Riga Mu Gidan Gaskiya Yana da Shekaru 68

  • Tsohon shugaban kasar Zambia, Edgar Lungu, ya rasu yana da shekaru 68, kamar yadda jam’iyyarsa ta sanar cikin wani jawabi
  • Lungu ya jagoranci Zambia na tsawon shekara shida (2015 zuwa 2021), kafin ya fadi zabe a hannun shugaba mai ci, Hakainde Hichilema
  • A wani bidiyo, ’yarsa Tasila Lungu ta bayyana cewa tsohon shugaban kasa ya yi fama da jinya a 'yan makonnin da suka gabata, kafin ya rasu a wani asibiti a kasar Afirka ta Kudu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Zambia - Tsohon shugaban ƙasar Zambia, Edgar Chagwa Lungu, ya riga mu gidan gaskiya bayan fama da jinya yana da shekaru 68 a duniya.

Jam'iyyarsa ta Patriotic Front ta tabbatar da rasuwar Lungu, wanda ya shugabanci ƙasar Zambia na tsawon shekaru shida daga 2015 zuwa 2021.

Marigayi tsohon shugaban Zambia, Edgar Lungu.
Tsohon shugaban ƙasar Zambia, Edgar Lungu ya kwanta dama Hoto: @MWebantu
Asali: Twitter

A cewar rahoton BBC, Lungu ya rasu ne da safiyar Alhamis, 5 ga Yuni, 2025, bayan samun kulawa ta musamman a wani asibiti a Pretoria da ke ƙasar Afirka ta Kudu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An tabbatar da rasuwar tsohon shugaban Zambia

‘Yarsa, Tasila Lungu-Mwansa, ta bayyana hakan a cikin wani bidiyo da aka yada a kafafen sada zumunta, rahoton Leadership.

A lokacin mulkin Shugaba Michael Sata, Lungu ya rike mukaman ministan shari’a da kuma ministan tsaro.

Bayan rasuwar Sata a watan Oktoba 2014, jam’iyyar Patriotic Front ta zaɓi Lungu a matsayin ɗan takara a taronta da aka gudanar a Kabwe.

Jam'iyyar ta tsaida Lungu a matsayin wanda zai fafata a zaben cike gurbi, inda ƴan Zambia suka zaɓi wanda ya ƙarisa wa'adin marigayi Sata.

Tarihin siyasar Marigayi Edgar Lungu

A wannan zaben, Lungu ya lallasa dan takarar adawa Hakainde Hichilema da kyar, inda ya kama aiki a matsayin shugaban kasa a ranar 25 ga Janairu, 2015.

An zabi Edgar Lungu a matsayin shugaban kasa na cikakken wa’adi a zaben watan Agusta 2016, ya sake kayar da Hakainde Hichilema da kyar.

Marigayi Lungi ya sha gwagwarmaya a siyasa.
Kasar Zambia ta rasa tsoshon shugabanta, Edgar Lungu bayan jinya a asibiti Hoto: @HHichilima
Asali: Twitter

Hichilema ya fara kin amincewa da sakamakon zaben, inda ya shigar da kara a kotun kundin tsarin mulki domin neman soke sakamakon.

Sai dai, a ranar 5 ga Satumba, 2016, kotun ta yi watsi da karar tare da tabbatar da nasarar Lungu.

An rantsar da shi a karo na farko a matsayin shugaban kasa mai cikakken wa’adi a ranar 13 ga Satumba, 2016.

A shekara ta 2021, Lungu ya sha kaye a hannun tsohon dan adawa, Hakainde Hichilema wanda ya fafata da shi a zaben 2015 da 2016.

Fitaccen marubucin Kenya ya rasu

A wani rahoton, kun ji cewa shahararren marubucin nan ɗan ƙasar Kenya, Ngũgĩ wa Thiong’o, ya riga mu gidan gaskiya yana da shekaru 87 a duniya.

Marigayin ya shahara a matsayin marubuci mai tsantsar salo na adabin Afirka, tare da kirkirar litattafan yara da kuma bayyana rashin jin dadinsa kan rashin daidaito da zalunci.

A watan Maris na 2024, aka samu labarin cewa marigayin na fama da cutar ƙoda kuma yana rayuwa shi kaɗai tare da kulawar jami’an lafiya a gidansa da ke California a Amurka.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262