Ramadan: Saudiyya Ta Tuna da Kano, Ta Yi Mata Goma Na Arziki, Abba Ya Yi Godiya

Ramadan: Saudiyya Ta Tuna da Kano, Ta Yi Mata Goma Na Arziki, Abba Ya Yi Godiya

  • Yayin da ake cikin wani hali a Najeriya, Saudiyya ta tuna da jihar Kano kan tallafin abinci ga marasa karfi
  • Gidauniyar Sarki Salman Ibn AbdulAziz ta ba da kayan abinci ga gidaje akalla 2,000 a kananan hukumomi takwas a jihar
  • Mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdussalam Gwarzo ya yabawa Gidauniyar da wannan taimako

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Gidauniyar Sarkin Saudiyya, Salman Ibn AbdulAziz ta raba kayan abinci ga gidaje fiye da 2,000 a jihar Kano.

Gidauniyar ta raba kayan abincin ne musamman ga mutanen nasu bukata ta musamman a kananan hukumomi takwas da ke jihar.

Saudiyya ta gwangwaje 'yan jihar Kano da kayan tallafi saboda Ramadan
Gidauniyar Sarki Salman na Saudiyya ta raba kayan abinci a Kano. Hoto: Abba Kabir Yusuf, Salman Ibn AbdulAziz.
Asali: Facebook

Wane nau'in abinci aka raba a Kano?

Kara karanta wannan

An garkame shugaban kungiyar 'yan kwadago, ana zargin ya karkatar da kayan tallafi

Shugaban Gidauniyar, Abdulrahman Ibn AbdulAziz Al-Zaben ya ce sun yi hakan ne ga marasa karfi domin rage musu radadi a wannan wata na Ramadan.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce kayan da aka raba sun hada da kilo 25 na shinkafa da wake da kuma garri kilo hudu da sauran kayan abinci, cewar Daily Trust.

Wannan rabon abincin ya zo a dai-dai lokacin da ake cikin wani hali na matsin tattalin arziki a Najeriya.

Gwamnatin Kano ta yi godiya da tallafin

Yayin da ya ke jawabi, mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdussalam Gwarzo ya godewa Gidauniyar da ta tuna da jihar a wannan yanayi.

Darakta-janar na hukumar NEMA, Zubaida Umar ta yabawa Gidauniyar kan wannan taimako da ta yi, Leadership ta tattaro.

Zubaidah wacce ta samu wakilcin daraktan ayyukan na musamman a hukumar NEMA, Fatima Kashim ta ce taimakon ya zo a dai-dai lokacin da ake buƙata.

Kara karanta wannan

AYM Shafa: Attajiri ya ware makudan kudi ga iyalan wadanda suka rasu wajen karbar zakkah

Wannan na zuwa ne bayan Gwamna Abba Kabir na jihar Kano ya ware biliyoyin kudi domin ciyar da mutane a watan Ramadan.

Dangote ya raba kayan abinci a Kano

A baya, mun ruwaito muku cewa Gidauniyar Alhaji Aliko Dangote ta sanar da raba kayan abinci ga al'umma a jihar Kano.

Gidauniyar ta ce a kullum ta na ciyar da mutane 10,000 a wannan wata na Ramadan domin saukaka musu wahalar da ake ciki.

Asali: Legit.ng

Online view pixel