Shugaba Tinubu Ya Roki ’Yan Najeriya Da Ke Amurka Su Dawo Gida Don Kawo Ci Gaba

Shugaba Tinubu Ya Roki ’Yan Najeriya Da Ke Amurka Su Dawo Gida Don Kawo Ci Gaba

  • Yayin da ya ke ci gaba da tattaunawa da ‘yan Najeriya a ketare, Bola Tinubu ya roke su da su dawo Najeriya
  • Tinubu ya bayyana haka ne yayin da ya ke ganawa da ‘yan Najeriya a birnin New York na Amurka
  • Ya ce a yanzu an samu ci gaba sosai a kasar inda ya bukace su da su manta da wahalhalun baya

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

New York, Amurka – Shugaba Bola Tinubu ya roki ‘yan Najeriya da ke kasashen ketare da su dawo Najeriya.

Tinubu ya bayyana haka ne yayin da ya ke ganawa da ‘yan Najeriya a birnin New York na Amurka.

Tinubu ya roki 'yan Najeriya a Amurka su dawo gida
Tinubu Ya Yi Wa ’Yan Najeriya da Ke Amurka Alkawari. Hoto: Bola Tinubu Ahmed.
Asali: Facebook

Meye Tinubu ya roki 'yan Najeriya a Amurka?

Shugaban ya bayyana musu cewa a yanzu fa an samu ci gaba a najeriya za su iya dawowa don taimakawa a bunkasa tattalin arziki, Vanguard ta tattaro.

Kara karanta wannan

Sauki ya zo: Shinkafa ta sauka a Arewa, buhun masara N20,000 a wata jiha

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya bukace su da su sauya tunani a kan Najeriya kamar a da, su zo kasar don amfana da bunkasar tattalin arziki da kuma damarmaki a kasar.

Ya ce:

“Zan ba ku misali daidai da ku, a baya na zauna a kasar waje, a irin halin da ku ke ciki, ku na bukatar sauya tunani wanda ya zama dole.
“Ku saka a cikin ranku a wannan dare, Najeriya gida ne da ke da damarmaki na kasuwanci masu yawa.”

Tinubu ya yi alfahari da irin ci gaban da ake samu a Najeriya ta bangarori da dama da ya jawo wa kasar ci gaba, cewar Tribune.

Wane alkwari Tinubu ya musu?

Ya bayana damar da ake da su yanzu a Najeriya inda ya bukace su da su zama masu ba da gudumawa a ko wane bangare.

Kara karanta wannan

Jirgi ya Kama Ci da Wuta Za Ayi Tafiya, Gwamna da Hadimansa Sun Tsira Daga Hadari

Ya kara da cewa:

“Ina alfahari da ku ganin yadda ake yabonku da da’a yayin da ku ke zaune a wadannan kasashe.
“Amma, mu na bukatarku a gida, Najeriya ta iso inda ake bukata, ku manta da wahalhalun da su ka faru a baya, yanzu an samu sauyin shugabanci.”

Remi Tinubu ta roki ‘yan Najeriya a ketare su dawo gida

A wani labarin, Uwar gidan shugaban kasa, Remi Tinubu ta roki ‘yan Najeriya da ke kasashen ketare da su dawo gida.

Remi ta bayyana haka ne yayin taron bunkasa tattalin arziki a birnin York a ranar 18 ga watan Satumba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.