Jihar Zamfara
Gwamnna jihar Zamfara Dauda Lawal Dare ya sanar da ranar Laraba, 19 ga watan Yuli, a matsayin ranar hutu a jihar domin murnar zagayowar shekarar musulinci.
Ana zargin 'yan sanda da kuma gwamnatin jihar Zamfara da kama motar shugaban jam'iyyar APC a jihar bisa wasu dalilai da ba a bayyana ba ya zuwa yanzu tukuna.
Dakarun sojoji a jihar Zamfara sun fattaki ƴan bindiga tare da ceto wasu mutum tara da suka yi garkuwa da su a ƙauyen Mailere cikin ƙaramar hukumar Bukkuyum.
Bello Matawalle, tsohon gwamnan Zamfara ya kara kokarin kwace mulki daga hannu gwamna Dauda Lawal a gaban kotun zaɓe, ya gabatar da shaidu 19 ranar Jumu'a.
Rundunar sojin Najeriya ta gargaɗi 'yan ta'adda da sauran 'yan bindigan daji musamman a Arewa maso Yamma da su miƙa wuya ko kuma dakaru su aika su barzahu.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya bayyana cewa ya gaji gwamnati ba tare da samun ko sisin kwabo ba a lalitar gwamnatin jihar, bayan tulin bashi a jihar
Gwamnatin jihar Kebbi ƙarkashin gwamna Dakta Nasir Idris ta samu nasarar ceto mutane 30 da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su a karamar hukumar Danko-Wasagu.
Babban hafsan sojin Najeriya, Manjo Janar Taoreed Lagbaja ya bukaci gwamnonin Arewa maso Yamma su cire hannunsu a harkar 'yan bindiga don ba su daman dakile su.
Babban hafsan tsaron ƙasar nan, CDS, Manjo Janar Christopher Musa, ya shiga taron sirri da gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal a hedkwatar tsaro ta ƙasa Abuja.
Jihar Zamfara
Samu kari