Siyasar Najeriya
Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi ya zama sabon shugaban ƙungiyar gwamnonin jam'iyyar PDP. Gwamnan Siminalayi Fubara na jihar Rivers ya zama sabon mataimaki.
Sabon gwamnan jihar Taraba, Dr. Kefas Agbu, ya yi shirin bincikar gwamnatin da ya gada ta Darius Ishaku. Gwamnan ya ce ba zai ƙasa a guiwa ba wajen binciken.
Gwamnatin jihar Kogi ta bayyana cewa wasu da ake zaton 'yan daban siyasa ne sun farmaki ayarin gwamna Yahaya Bello na tsakar ranar Asabar a hanyar zuwa Lokoja.
Gwamnan jihar Zamfara, Lawal Dauda, ya bayyana yadda tsohuwar gwamnatin Matawalle ta siyo manyan motoci na alfarma na biliyan N2.79bn amma ko ɗaya bai bari ba.
Tsohon gwamnan jihar Ribas wanda ya sauka ranar Litinin da ta shige, Nyesom Wike, ya ce ko kaɗan bai fara tunanin sauya sheka daga PDP zuwa jam'iyyar APC ba.
Tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani ya zargi jam'iyyar APC a jihar Ƙaduna da rashin iya gudanar da mulki, a shekara takwas da ta kwashe a mulkin jihar.
Gwamna Seyi Makinde ya bayyana cewa shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, na bukatar goyon bayan kowane ɗan Najeriya a daidai wannan lokaci mai matuƙar wahala.
Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC ta tabbatar wa Kotun sauraron korafe-korafen zaben gwamnan Kaduna cewa Malam Uba Sani ne ya samu nasara a watan Maris.
Gwamnonin ci gaba na jam'iyyar APC sun nuna damuwarsu kan yadda yan kasuwa suka ƙara farashi nan take bayan kalaman sabon shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.
Siyasar Najeriya
Samu kari