Wike: Na San Peter Obi Ba Zai Kai Labari Ba Domin Masoyansa Ba Su San Siyasa Ba

Wike: Na San Peter Obi Ba Zai Kai Labari Ba Domin Masoyansa Ba Su San Siyasa Ba

  • Ministan Abuja ya bayyana cewa tun usuli ya san cewa Peter Obi ba zai iya lashe zaben shugaban ƙasa a watan Fabrairu ba
  • Nyesom Wike, tsohon gwamnan jihar Ribas ya ce magoya bayan Obi ba su san yanayin siyasar Najeriya ba
  • Kalaman ministan na zuwa ne kwana ɗaya tal bayan Kotun sauraron karar zaben shugaban ƙasa ta yanke hukuncinta

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

FCT Abuja - Ministan babban birnin tarayya (FCT Abuja), Nyesom Wike, ya yi ikirarin cewa magoya bayan Peter Obi, ɗan takarar shugaban kasa na Labour Party, ba su san siyasa ba.

Wike, tsohon gwamnan jihar Ribas kuma babban jigon PDP ya yi wannan ikirarin yayin hira da gidan talabijin na Channels ranar Alhamis, 7 ga watan Satumba, 2023.

Ministan Abuja, Nyesom Wike.
Wike: Na San Peter Obi Ba Zai Kai Labari Ba Domin Masoyansa Ba Su San Siyasa Ba Hoto: Nyesom Wike
Asali: Facebook

Kalaman Ministan na zuwa ne awanni 24 bayan Kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaben shugaban ƙasa ta tabbatar da nasarar shugaban ƙasa, Bola Tinubu a zaben 2023.

Kara karanta wannan

To Fa: Atiku Abubakar Ya Shiga Sabuwar Rigima Yayin da Yake Shirin Ɗaukaka Kara Zuwa Kotun Ƙoli

Jaridar The Nation ta rahoto Wike na cewa:

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

"Tun farko dama na san Peter Obi ba zai samu nasara a zaɓe ba, bari na faɗa muku gaskiya, ni bana ɓoye-ɓoye, a ganina zaɓen nan da ya wuce ya yi zafi, jinjina ga INEC."
"Eh to a matsayinsa na matashi, wasu mutane zasu so a ce shi ne ya samu nasara, to amma ku duba yadda ƙuri'un da aka kaɗa suka nuna. An samu yanayin sauyi na zamani, matasa sun gaji."
"Saboda haka a tunaninsu kawai su dangwala wa Obi kuri'unsu domin shi ne matashi idan aka kwatanta da sauran 'yan takara. Amma abinda ba su sani ba, ba haka siyasar Najeriya take ba."

Wike ya ƙara da cewa matasan da ke goyon bayan Peter Obi ba su san siyasa ba domin ba su san cewa kabilanci da addini na taka rawa a siyasar Najeriya ba.

Kara karanta wannan

Hukuncin Kotu: An Bayyana Wani Muhimmin Dalili Da Zai Sanya Shugaba Tinubu Ya Cigaba Da Nasara Akan Atiku Da Peter Obi

A cewarsa, cancantar ɗan takara kaɗai ba zata kai shi ga nasara ba a yanayin siyasar da ake murza a wa a ƙasar nan.

Adamawa: Abinda Ya Sa Muka Sa Hoton Gwamna a Buhunan Shinkafa, Amos

Kuna da labarin Gwamnatin jihar Adamawa ta yi ƙarin haske kan dalilin sanya hoton gwamna Fintiri a jikin buhunan Shinkafar tallafi

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya tura wa jihohi kuɗi da kayan abinci domin raba wa yan Najeriya su rage radaɗin cire tallafin fetur.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262