Siyasar Najeriya
Mamba mai wakiltar Pankshin ta Arewa a majalisar dokokin jihar Filato, Gabriel Dawang, a ranar Talata, 21 ga watan Nuwamba, ya zama sabon shugaban majalisar.
Fadar shugaban ƙasa ta ɗora alhakin halin da dimokuraɗiyyar ƙasar nan take ciki a kan tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo, inda ta ce shi ya kawo ta ƙasar nan.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana kwarin guiwar cewa shi ne zai sake lashe zaben da kotu ta bada umarnin a sake shiryawa a kananan hukumomi uku.
Tsohon mai magana da yawun kwamitin kamfen Atiku/Okowa na PDP, Daniel Bwala ya soki tsige Gwamna Celeb Mutfwanga na jihar Filato da kotun ɗaukaka kara ta yi.
Fadar shugaban kasa ta musnata zarge-zargen PDP da ɗan takararta na shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ta ce Tinubu ba ya tsoma baki a harkokin shari'a.
Daniel Bwala, tsohon mai magana da yawun kwamitin yaƙin neman zaben Atiku/Okowa na PDP ya ayyana INEC a matsayin babbar matsalar zaɓen 2023 da aka gama.
Garba Muhammad Datti, ya yi hasahen cewa nan bada jimawa ba karamin ministan tsaro, Bello Matawalle, zai dawo da nasarar da ya samu a zaben jihar Zamfara.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya zargi APC mai mulki da kokarin kwace jihohin da jam'iyyun adawa ke mulki da ƙarfin magudi ko a Kotu.
An buƙaci ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar da ya ceto jam'iyyar a zaɓen 2027, inda aka gaya masa hanya mafi sauƙi da zai yi hakan.
Siyasar Najeriya
Samu kari