Hukumar yan sandan NAjeriya
Rundunar yan sandan jihar Kaduna ta samu nasarar cafke wasu mutum biyu da ake zargi da aikata laifin sace janareto da batiri mai amfani da hasken rana a masallaci.
Yan bindiga sun sake tafka ta'asa a jihar Benue a wani sabon harin ta'addanci da suka kai. Yan bindigan a yayin harin sun sace shugaban karamar hukuma.
Kwamishinan yan sandan jihar Kano ya bayar da sabon umarni ga jami'an yan sandan jihar, biyo bayan hukuncin kotun koli da ya tabbatar da nasarar Gwamna Abba.
Wasu sojoji guda biyu sun samu nasarar kama wani mutum da ya ke amfani da kakin soja wajen damfarar mutane a Nasarawa. Sun kama shi ne a garin Awe da ke jihar.
Tsohon mataimakin Sifetan 'yan sanda a Najeriya, Okoye Ikemefuna ya riga mu gidan gaskiya a ranar 7 ga watan Janairun wannan shekara bayan fama da jinya.
Yayin da ake shirin yanke hukuncin Kotun Koli a jihohin Kano da Zamfara da Bauchi da sauran jihohi 5, an tsaurara jami'an tsaro kan hukuncin a jihohin.
Dan Majalisar jihar Plateau, Hon. Adamu Aliyu ya bankado yadda ake korar Hausawa a yayin tantance masu neman aikin dan sanda a karamar hukumar Jos ta Arewa.
Rundunar ‘yan sandan jihar Gombe a ranar Laraba ta gurfanar da wasu da ake zatton masu fataucin mutane ne bayan sun siyar da wani jariri kan kudi Naira 400,000.
Wasu miyagun yan bindiga sun ci karensu babu babbaka a wani sabon harin ta'addanci da suka kai a jihar Katsina. Miyagun yan bindigan sun halaka mutum tara.
Hukumar yan sandan NAjeriya
Samu kari