Hukumar yan sandan NAjeriya
Rundunar yan sandan babban birnin tarayya Abuja, sun bayyana rahoton garkuwa da mutane a rukunin gidaje na River Park, Abuja a matsayin kanzon kurege.
Wasu tsagerun yan bindiga sun yi ajalin jami'an hukumar ɗan sanda ɗaya yayin da suka kai hari caji ofis a wani kauyen karamar hukumar Batsari da je jihar Katsina.
Ma'aikatan wani otel da ke Yola sun gano gawar wata mata cikin yanayi mara kyau bayan wani mutum da suka taho otel din tare ya fita da cewa zai dawo ba da dadewa ba.
Akalla yara 10 ne suka samu munanan raunuka bayan wani abin fashewa ya jikkata yaran a kauyen Kidandan da ke karamar hukumar Giwa a jihar Kaduna.
Rundunar yan sanda ta tabbatar da kama kasurgumin ɗan garkuwa da mutane, Chinaza Phillip, wanda ya yi ƙauren suna wajen satar mutane a birnin tarayya Abuja.
Dan majalisar dokokin jihar Kogi ya tabbatar da rasa rayuka biyu da kadarorin miliyoyin naira a wani rikici da ya ɓalle tsakanin kauyuka 2 a karamar hukumar Ankpa.
Rundunar yan sandan Najeriya reshen jihar Bauchi ta yi nasarar kama wani dalibin jami'ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi mai suna Mike Habila da bindigu.
Miyagun yan bindiga dauke da makamai da ke kai hare-haren ta'addanci sun raba mazauna kauyuka 10 na karamar hukumar Giwa ta jihar Kaduna da matsugunansu.
Rundunar yan sanda ta bayyana ikirarin cewa hukumar tsaron ta taba daukar kasurgumin dan bindiga, Bello Turji aiki a matsayin karya. ACP Adejobi ne ya karyata hakan.
Hukumar yan sandan NAjeriya
Samu kari